Abin da Ya Faru a Qatar bayan Iran Ta Harba Makami Mai Linzami kan Sojojin Amurka

Abin da Ya Faru a Qatar bayan Iran Ta Harba Makami Mai Linzami kan Sojojin Amurka

  • Gwamnatin Qatar ta ce na'u'rorin kakkaɓo makamai sun yi nasarar daƙile harin da Iran ta yi nufin kai wa sansanin sojin Amurka na Al Udeid
  • Ma'aikatar tsaron Qatar ta bayyana cewa babu wanda ya ji rauni ko rasa rai sakamakon harin, wanda Iran ta kai da nufin ramuwar gayya
  • Wannan ma zuwa ne kwanaki kaɗan bayan Amurka ta kai hari kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lamarin da ya ja hankalin duniya

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Qatar - Gwamnatin Qatar ta bayyana cewa na'urorin tsaron sama sun yi nasarar daƙile makamin da Iran ta harbo kan sansanin sojin Amurka na Al Udeid da ke ƙasarta.

Ma’aikatar Tsaron Qatar ta sanar da cewa babu wanda ya samu rauni ko ya rasa rai sakamakon harin wanda Iran ta kaddamar da nufin ramuwar gayya kan Amurka.

Kara karanta wannan

Iran ta kaddamar da harin ramuwar gayya kan Amurka

Qatar ta kakkaɓo makamin da Iran ta harbo.
Qatar ta yi Allah wadai da harin da Iran ta kai kan sansanin sojin Amurka Hoto: Getty Image
Source: Twitter

Ta bayyana haka ne a wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, wanda a baya aka fi sani da Twitter ranar Litinin, 23 ga watan Yuni, 2025.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Qatar ta daƙile harin da Iran ta kai kan sojin Amurka

Ma'aikatar tsaron Qatar ta kara da cewa jajircewar dakarun sojin sama da kuma matakan kariyar da ƙasar ta ɗauka ne suka taimaka wajen daƙile harin.

Har ila yau, ma’aikatar ta ƙara da cewa Qatar da sararin samaniyarta suna cikin tsaro, kuma dakarun tsaron ƙasar sun shirya tsaf domin tunkarar kowanne irin barazana.

Wannan dai na zuwa ne bayan Majalisar Tsaron Iran ta bayyana cewa harin makami mai linzami da ta kai sansanin sojin Amurka na Qatar ba shi da nufin taɓa fararen hula.

“Wannan matakin ba barazana ba ce ga ƙawarmu Qatar ko jama'arta. Jamhuriyar Musulunci ta Iran na nan daram wajen ƙarfafa dangantakar zumunci da ke tsakaninta da Qatar.”

Kara karanta wannan

Yaki da Isra'ila: Jerin kasashen da suka gargadi Trump bayan kai hari a Iran

Qatar da nuna ɓacin ranta da matakin Iran

Amma a nata ɓangaren, Qatar ta yi Allah wadai da harin tana mai cewa hakan cin mutunci ne ga ƙasar.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje ta Qatar, Majed al-Ansari, ya bayyana harin da dakarun juyin juya halin Iran IRGC a matsayin wanda ya karya dokar ƙasa da ƙasa.

Yadda aka ga makamin da Iran ta harbo a Qatar.
Gwamnatin Qatar ta yi Allah wadai da harin Iran kan sansanin sojin Amurka Hoto: Getty Images
Source: Getty Images
"Wannan hari ya karya dokar ƙasar Qatar da sararin samanta, haka kuma ya saɓa wa dokar Majalisar Ɗinkin Duniya."
"Mu a Ƙasar Qatar muna da ‘yancin maida martani kan wannan ƙeta dokar da aka yi bisa ga ka’idojin doka ta ƙasa da ƙasa,” in ji al-Ansari a cikin wata sanarwa.

Ya ƙara da cewa jami'an tsaron Qatar sun samu nasarar daƙile harin kuma sun kankaɓo makaman Iran da suka nufi sansanin sojin Amurka a ƙasar.

Kasashe sun shirya taimakon Iran

A wani labarin, kun ji cewa Rasha ta yi ikirarin cewa ƙasashen da dama sun nuna a shirye suke su bai wa Iran makaman nukiliya bayan harin da Amurka ta kai.

Kara karanta wannan

Amurka ta risina, ta roki China ta shawo kan Iran a kan rufe hanyar Hormuz

Mataimakin shugaban majalisar tsaro na Rasha, Dmitry Medvedev, ya bayyana cewa a halin yanzu, ƙasashen da a baya ba su goyon bayan Iran, sun canza shawara.

Medvedev ya ce duk da hare-haren ba su yi mummunan ɓarna sosai ba, akwai yuwuwar Iran ta ci gaba da shirinta na mallakar malamin nukiliya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262