Iran Ta Kara Kai Zafafan Hare Hare, Ta Harba Makamai Masu Linzami kan Isra'ila

Iran Ta Kara Kai Zafafan Hare Hare, Ta Harba Makamai Masu Linzami kan Isra'ila

  • Ƙasar Iran ta sanar da ƙara kai hare-hare Isra'ila yayin da rikici tsakanin kasashen biyu ke ƙara ta'azzara
  • A wata sanarwa da gidan talabijin na gwamnatin Iran ya fitar, ta ce ƙasar ta harba jirage marasa matuƙa da makamai masu linzami
  • Har yanzu babu wata sanarwa daga Isra'ila kan waɗannan hare-hare da Iran ta tabbatar da kai wa a yau Talata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Iran - Ƙasar Iran ta ƙaddamar da wani sabon jerin hare-haren jiragen yaki marasa matuki da makamai masu linzami kan Isra’ila.

An ruwaito cewa wannan shi ne zai zama karo na 10 a jerin hare-haren soji da ƙasar Iran ta kai Isra'ila wanda ta sanya wa suna “Operation Honest Promise 3."

Iran ta sake harba makamai kasar Isra'ila.
Iran ta sanar da kara kai hare-hare kan Isra'ila Hoto: @Iran
Source: Twitter

Gidan talabijin na gwamnati a Tehran, babban birnin Iran ne ya tabbatar da kai sababbin hare-haren, kamar yadda tashar DW ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Yaki ya barke tsakanin Rasha da Ukraine, makami mai linzami ya kashe mutane 15

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ƙasar Iran ta kai sababbin hare-hare a Isra'ila

An tabbatar da hare-haren na baya-bayan nan a ranar Talata, 17 ga watan Yuni, 2025 a daidai lokacin da rikicin tsakanin ƙasashen biyu ya shiga rana ta biyar a jere.

Gidan talabijin na gwamnatin ya bayyana cewa Rundunar Musulunci ta Iran (IRGC) ce ta jagoranci kai sababbin hare-haren, wadanda ta ce an kai su ne kan biranen Isra'ila.

Kamfanin dillancin labarai na Tasnim, wanda ke da kusanci da gwamnatin Iran, shi ma ya tabbatar da an kai waɗannan sababbin hare-hare.

Makaman da Iran ta yi amfani da su

Rahoton ya kara da cewa a wannan karon, Iran ta harba jirage marasa matuƙa da rokoki duk a wani bangare na ramuwar gayya da Iran ke ci gaba da yi.

Tun farko dai Isra'ila ta fara kai hari Iran, inda ta kashe manyan hafsoshin soji da masana nukiliya, tare da ɗaruruwan fararen hula.

Kara karanta wannan

Iran da Isra'ila na cigaba da asarar rayuka yayin da musayar wuta yayi kamari

Bayan haka ne Iran ta fara kai hare-haren ramuwar gayya kan Isra'ila, ita ma ta kashe mutane sama da 20, rahoton CNN.

Jagororin Iran da Isra'ila.
Iran ta ci gaba da kai hare-hare masu zafi kan Isra'ila Hoto: Getty Image
Source: Getty Images

Wane illa hare-haren Iran suka yi wa Isra'ila?

A halin yanzu dai babu wata sanarwa kai tsaye daga hukumomin Isra’ila kan sababbin hare-haren da Iran ta ce ta kai.

Sai dai wadannan hare-haren na kara dagula rikicin da ke tsakanin Iran da Isra’ila, yayin da manyan ƙasashe. duniya da yankin Gabas ta Tsakiya ke sa ido sosai kan lamarin.

Har kawo yanzu ba a tantance yawan barnar da hare-haren suka haddasa ko adadin asarar rayuka ba.

Iran ta lalata wata matatar man Isra'ila

A wani rahoton, kun ji cewa hukumar da ke kula da matatar mai a Haifa ta ƙasar Isra’ila, ta sanar da dakatar da dukkan ayyukanta bayan wani harin roka da Iran ta kai.

Rahotanni sun nuna cewa Iran ta samu nasarar lalata muhimman ɓangarori a matatar, lamarin da aya tilastawa kamfanin da ke kula da ita dakatar da aiki.

Kamfanin ya ce rokokin da Iran ta harba sun lalata tashar wutar lantarki da matatar ke amfani da ita wajen sarrafa man fetur.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262