Saudiyya Ta Fitar da Sanarwa, Ta Bayyana Ranakun Hawa Arafah da Babbar Sallah

Saudiyya Ta Fitar da Sanarwa, Ta Bayyana Ranakun Hawa Arafah da Babbar Sallah

  • Hukumomin Saudiyya sun bayyana cewa an ga jinjirin watan Dhul Hijjah a yau Talata, 29 ga watan Dhul Qa'adah, 1446 daidai da 27 ga watan Mayu
  • A sanarwar da hukumomin suka fitar da yammacin nan, za a yi hawan Arafah a ƙasar a ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2027
  • Haka nan kuma musulmi a ƙasar Saudiyya za su yi hawan idin layya watau Eid El Adha ranar Juma'a, 10 ga watan Dhul Hijjah daidai da 6 ga watan Yuni

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Saudi Arabia - Hukumomi a kasar Saudiyya sun tabbatar da ganin jinjirin watan Dhul Hijjah a yau Talata, 29 ga watan Dhul Qa'adah, 1446H daidai da 27 ga watan Mayu, 2025.

Hakan dai na nufin gobe Laraba, 28 ga watan Mayu, 2025 zai kama 1 kenan ga watan Dhul Hijjah, 1446H, wata na 12 a jerin watannin kalandar addinin Musulunci.

Kara karanta wannan

Eid El Adha: Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya sanar da ranar babbar sallah a Najeriya

Duban wata.
An ga jinjirin watan Babbar Sallah a ƙasar Saudiyya Hoto: Inside The Haramain
Source: Twitter

Hakan dai na kunshe ne a wata sanarwa da aka wallafa a shafin hukumar kula da manyan masallatai biyu masu daraja da alfarma Inside The Haramai a Facebook.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ranakun Arafah da babbar sallah a Saudiyya

A cewar sanarwar, alhazai za su yi hawan Arafah a ranar Alhamis, 9 ga watan Dhul Hijjah, wanda zai yi daidai da 5 ga watan Yuni, 2025.

Sanarwar ta bayyana cewa sallar layya watau Eid El Adha za ta kama ranar 6 ga watan Yuni, 2025 daidai da 10 ga watan Dhul Hijjah, 1446H.

Wannan wata na Dhul Hijjah na da matuƙar daraja da ƙima a addinin musulunci, a cikinsa ne musulmi ke yin ibadar aikin hajji, ɗaya daga cikin rukunan addinin.

Haka zalika a wannan wata ne musulmi daga kowane yanki a duniya suke yin sallar layya, watau babbar sallah (Eid El Adha), ɗaya daga cikin idi biyu da musulmai ke yi a kowace shekara.

Kara karanta wannan

Hajjin bana: Mahajjaciyar Najeriya ta rasu a asibitin Makkah

Alhazai.
Za a yi hawan Arafah ranar Alhamis, 5 ga watan Yuni, 2025 Hoto: Inside The Haramain
Source: Facebook

Sanarwar da Saudiyya ta fitar kan ganin wata

Sanarwar da hukumomin Saudiyya suka fitar ta ce:

"An ga jinjirin wata a Saudiyya, gobe Laraba, 28 ga watan Mayu, 2027 za ta kama 1 ga watan Dhul Hijjah, 1446H.
"Ranar hawa Arafah kuma za ta kama ranar Alhamis, 9 ga watan Dhul Hijjah, 1446 wanda zai zama daidai da 5 ga watan Yuni, 2025.
"Sai kuma Eid El Adha watau sallar layya, ita kuma za a yi hawan idin a ranar Juma'a ta makon gobe, 6 ga watan Yuni, 2025 daidai 10 ga watan Dhul Hijjah.

Wannan sanarwa dai ta tabbatar da cewa watan Dhul Qa'adah ya kare daga yau Talata, sannan gobe Laraba ne 1 ga watan Dhul Hijjah, 1446H.

Kasar Saudiyya ta naɗa limamin Arafah

A wani labarin, kun ji cewa hukumomi a Saudiyya sun sanar da cewa Sheikh Saleh bin Abdullah Al Humaid ne zai yi huɗuba a tsayuwar Arafah ta shekarar 1446 bayan Hijira.

Kara karanta wannan

Boko Haram ta ji dadin farmakin sansanin sojoji, ta sake kai hari Borno

Sheikh Saleh zai gabatar da huɗubar wannan rana mai matuƙar daraja ta Arafah daga masallacin Namira a ranar Alhamis, 9 ga watan Dhul Hijjah, 1446H.

Malamin ya rike mukamai da dama a Saudiyya, ciki har da shugaban majalisar Shura a shekarar 1422 da shugaban babban kotun shari’a a 1430.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262