Saudiyya Ta Bayyana Ranar Karamar Sallah Bayan Samun Rahoton Kwamitin Ganin Wata

Saudiyya Ta Bayyana Ranar Karamar Sallah Bayan Samun Rahoton Kwamitin Ganin Wata

  • Hukumomin Saudiyya sun bayyana cewa ba a ga watan Shawwal ba bayan tawagar masu duba wata ba su ga watan a yau ba
  • Wannan na nufin a ranar Laraba, 10 ga watan Afrilu za a gudanar da Sallah karama a Saudiyya
  • Har yanzu ana dakon sakamakon ganin Shawwal a ranar Litinin, wanda fadar sarkin Musulmi ta ce za ta bayyana Talata a matsayin ranar Sallah idan an ga wata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Saudiyya - Hukumomin Saudiyya sun bayyana ranar Laraba a matsayin ranar sallah ƙarama.

A shafinta na haramain a X, tawagar ganin wata ba su ga watan Shawwal ba.

Kara karanta wannan

Azumi 30: Sarkin Musulmi ya sanar da ranar da za a yi Ƙaramar Sallah a Najeriya

Wannan na zuwa ne sakamakon gaza ganin jaririn watan Shawwal da tawagar duban wata su ka yi a Litinin ɗin nan.

Rashin ganin watan na nufin sallah ƙarama za ta kama ranar 10 ga watan Afrilu.

Hukumomin Saudiyya sun bayyana ranar Sallah
Saudiyya ta bayyana ranar Sallah Karama bayan samun rahoto. Hoto: Haramain
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ranar Larabar za ta zamo 1 ga watan Shawwal 1445A.H sannan kuma ana da labari an fara duban watan Shawwal a Najeriya

Sakamakon duba watan Sallah a Najeriya

Fadar Sarkin Musulmi ta umarci Musulman Najeriya su ci gaba da duban watan karamar Sallah a yau.

A sanarwar da Sakataren NSCIA Farfesa Ishaq Oloyede ya fitar ranar Lahadi, za a bayyana Talata 1 ga watan Shawwal idan an ga watan.

Akasin ganin watan na nufin za a yi sallah ranar Laraba, 10 ga watan Afrilu.

Yadda za a sanar da hukumomi ganin wata

Fadar mai martaba Sarkin Musulmin ta ce duk wanda ya ga watan zai iya tuntubarsu domin sanar da su.

Kara karanta wannan

Bayan gama duban wata, Saudiyya ta sanar da ranar idin ƙaramar sallah a 1445/2024

Ta cikin sanarwar da da fadar ta fitar, ta rubuta lambobin wayar da za a tuntube su domin sanar da ganin watan.

Yau Kwanaki 29 da fara azumi a duniya

A ranar 11 ga watan watan Maris ne Musulmin duniya suka ɗauki azumin watan Ramadan.

Yau Kwanaki 29 ke nan da fara azumin a sassan duniya daban-daban.

A kasashe irinsu Saudiyya, za su yi azumi 30 saboda rashin ganin watan Shawwal a ranar Litinin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel