Birnin New York Ta Bai Wa Musulmai Damar Kiran Sallah Ranar Juma'a Da Watan Ramadan

Birnin New York Ta Bai Wa Musulmai Damar Kiran Sallah Ranar Juma'a Da Watan Ramadan

  • A karshe al’ummar Musulmai za su samu su sarara bayan birnin New York ta ba su daman kirar salla a wasu zababbun lokuta a birnin baki daya
  • Magajin birnin New York, Eric Adams shi ya sanar da haka yayin ganawa da al’ummar Musulmai kan matsalar kiran salla a birnin
  • Sanarwar ta ba wa al’ummar Musulmai damar kiran salla a masallatai a ranar Juma’a da kuma watan Ramadan ba tare da neman izini ba

New York, Amurka - Birnin New York a Amurka ta ba da umarnin jiyar da kiran salla a wasu zababbun lokuta a masallatai na birnin baki daya.

Magajin birnin New York, Eric Adams shi ya bayyana haka a ranar Talata 29 ga watan Agusta inda ya ce hakan zai saka Musulmai su ji ana damawa da su.

Kara karanta wannan

Jami’in Dan Sanda a Adamawa Ya Sharbi Kuka Wiwi Bayan An Sallame Shi a Aiki, Bidiyon Ya Yadu

Birnin New York ta ba da damar kiran salla ga Musulmai a zababbun lokuta
Musulmai Za Su Sarara Yayin Da Birnin New York Ta Ba Da Damar Kiran Sallah Ranar Juma'a Da Watan Ramadan. Hoto: Muslim Relief.
Asali: Getty Images

Meye dokar ta ce kan kiran sallar Musulmai?

A sabuwar dokar, Adams ya ce za a jiyar da kiran sallah ba tare da Musulmai sun nemi izini ba daga hukumomi a ranakun Juma’a da kuma lokacin shan ruwa a watan Ramadan, cewar CNN.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Sanarwar ta ce jami’an ‘yan sanda za su yi aiki tare da masallatai don bin ka’idojin da aka tsara don tabbatar da karar lasifikan ya yi dai-dai da tsari.

Adams wanda ya ke tare da shugabannin Musulman birnin New York ya ce:

“Musulman birnin New York za su samu sararawa a matsayina na magajin birnin.”

Meye dalilin daukar matakin kiran sallar Musumai?

AP News ta tattaro Adams na cewa:

“An dauki tsawon lokaci ana samun rikitarwa a kan wadanne yankuna ne ba a barin a yi kiran sallah da lasifika.

Kara karanta wannan

Jaruma Lizzy Anjorin Ta Bar Musulunci, Ta Yi Gargadi Mai Tsauri a Bidiyo: "Ba Musulmin Da Ya Kare Ni Lokacin Da Ake Tsangwamata"

“A yau muna so mu kawo karshen wannan abu inda muke bayyana cewa masallatai na iya yin kiran sallah a bayyane a ranakun Juma’a da kuma watan Ramadan ba tare da sake neman izini ba,”

Indiya Ta Rufe Makaranatar Da Aka Ci Zarafin Dalibi Musulmi

A wani labarin, yayin da ake ta cece-kuce bayan ganin wani faifan bidiyo da wata malama ke cin zarafin dalibi Musulmi, hukumomi sun dauki mataki.

Hukumomi a kasar Indiya sun rufe makarantar da aka samu wannan cin zarafi tare da gurfanar da malamar don amsa tambayoyi.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.