Da dumi-dumi: Tsohon gwamnan Najeriya ya mutu a ranar bikin samun 'yancin kai

Da dumi-dumi: Tsohon gwamnan Najeriya ya mutu a ranar bikin samun 'yancin kai

  • Commodore Ibrahim Kefas (mai ritaya), tsohon gwamnan Delta da Cross River a mulkin soja, ya rasu a ranar Juma'a, 1 ga watan Oktoba
  • Marigayi Kefas wanda ya rasu yana da shekara 73 ya yi aiki a matsayin jagora a mulkin soja na marigayi Janar Sani Abacha
  • Kefas ya sha kaye a hannun dan takarar PDP, Danbaba Suntai, a jihar Taraba yayin zaben gwamna na 2007

A daidai lokacin da 'yan Najeriya suke bikin murnar ranar yancin kan kasarsu, sai ga wani labari mara dadi na wani mutuwa da ya zo a ranar Juma'a, 1 ga watan Oktoba.

Kamar yadda AIT News ta ruwaito, tsohon gwamnan na Cross River da Delta a mulkin soji, Commodore Ibrahim Kefas (mai ritaya), ya rasu a ranar Juma'a a wani asibitin Abuja yana da shekaru 73.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun cafke masu garkuwa da mutane 2 su na tsaka da amsar kuɗin fansa

Da dumi-dumi: Tsohon gwamnan Najeriya ya mutu a ranar bikin samun 'yancin kai
Tsohon gwamnan Najeriya ya mutu a ranar bikin samun 'yancin kai Hoto: AIT News
Asali: UGC

An binne marigayin daidai da koyarwar addinin Islama a wannan ranar.

Marigayi Kefas ya yi gwamnan soja na jihohin biyu tsakanin 1993 zuwa 1996 a zamanin mulkin soja na marigayi Janar Sani Abacha.

Shekaru bayan haka, Kefas ya tsaya takarar gwamnan Taraba a 2007 amma ya sha kaye a hannun dan takarar jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP), Danbaba Suntai.

Tsohon gwamnan mulkin soja, Ndubisi Kanu, ya rasu

A wani labarin, mun kawo cewa tsohon gwamnan jihohin Legas da Imo a zamanin mulkin soja, Rear Admiral Ndubisi Kanu (mai murabus) ya rasu yana da shekaru 77 a duniya.

Abokiyar huldar Kanu kuma mukusanciyarsa, Mrs Joe Okei-Odumakin ta tabbatar wa The Punch labarin a ranar Laraba.

Kanu, wadda tsohon shugaban kasar mulkin soja, Janar Murtala Mohammed ya nada cikin majalisar kolin sojoji a shekarar 1975, daga bisani ya zama mai rajin kare hakkin bil adama bayan barin aikin soja.

Kara karanta wannan

'Yan fashi sun afka wa coci domin sace kudi, sun daba wa mai gadi wuka a Abuja

Asali: Legit.ng

Online view pixel