Kwastam za ta fara amfani da 'Drone' wajen sintiri da kama haramtattun kayayyaki

Kwastam za ta fara amfani da 'Drone' wajen sintiri da kama haramtattun kayayyaki

  • Hukumar kwastam ta bayyana cewa, za ta fara amfani da jirage marasa matuki don aikwatar da ayyukanta
  • A cewar hukumar, amfani da fasahar zai taiamaka wajen saukake ayyukan sintiri a bakin iyakokin kasa
  • Hukumar kwastam na ci gaba da runtuma kamen haramtattun kayayyaki da ake shigo dasu Najeriya ba bisa ka'ida ba

Hukumar Kwastam ta Najeriya (NCS), ta ce nan ba da jimawa ba za ta tura jirage marasa matuka a Seme don yin sintiri mai inganci wajen duba ayyukan fasa kwabri a yankin kan iyaka, Daily Nigerian ta ruwaito.

Kodinetar Yanki na NCS, Modupe Aremu, Mataimakiyar Kwanturola Janar (ACG) na Kwastam, ta bayyana hakan a ranar Litinin 20 ga watan Satumba yayin ziyarar aiki zuwa Kwamitin Yankin Iyakokin Seme.

Kara karanta wannan

Shugaban kasa a 2023: Kudu ba za ta goyi bayan duk jam’iyyar da ta tsayar da dan arewa ba, in ji gwamnan APC

Kwastam za ta fara amfani da 'Drone' wajen sintiri da kama haramtattun kayayyaki
Modupe Aremu | Hoto: financialbusiness.com.ng
Asali: UGC

A cewarta, za a yi aikin kula da iyakokin ta hanyar zamani da amfani da jirage marasa matuka don tabbatar da cewa za a iya nazarin yankin game da abin da ke faruwa.

A kalamanta:

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

“Ziyarar yankin Seme shine karshen ziyarar da na yi a Zone A kuma dole ne in yaba wa dukkan yankunan, suna da sama da 80% na tattara kudaden shiga da NCS ke yi don haka ya kamata su ci gaba da yin kyakkyawan aiki.
"Tare da rangadin dukkan yankuna, na ga cewa duk jami'ai na kan kokari amma suna bukatar kara kaimi. Kuma ina gaya musu cewa ya kamata su yi tsammanin ziyarar ba -zata daga Mai Kula da Shiyya, don haka kada su sassauta kan aiki.
“Hakanan, kwangilar e-kwastam na N300bn wanda shine cikakken fasahar sarrafa kai wanda ake shirin fara aiwatar da Hadin Fasahar Bayanai da Sadarwa; idan ya kankama, za mu sami fasahar zamani, jirage marasa matuka suna sintiri kan iyaka.”

Kara karanta wannan

Jirgin yaki ya yi luguden wuta kan al’umman gari? Rundunar soji ta yi martani kan rahoton

Ta shaida cewa hukumar kwastam na kokarin rage mu'amalar mutum da wuraren sintiri don samar da cikakken aiki mai inganci.

Sojin ruwa sun kame buhunnan shinkafar kasar waje da aka shigo da ita Najeriya

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta NNSV, ta cafke mutane uku da ake zargi da fasa kwabrin buhunan haramtacciyar shinkafa guda 1,209 ta ruwa, Daily Nigerian ta kawo.

Wadanda ake zargin, Humble Edet, Christian Adebayo da Balle Philip sun shiga hannun jami’an NNSV ne da ke sintiri a nisan mil biyu na ruwa a yankin kudu maso gabas a Calabar.

Da yake yiwa manema labarai karin haske a tashar jirgin ruwan NNSV a ranar Litinin a Calabar, Kwamandan NNSV, Chiedozie Okehie, ya ce an kama wadanda ake zargin ne da laifin shigo da kayayyakin da aka haramta shigo dasu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya ya ruwaito cewa Okehie, ya samu wakilcin Babban Jami'in Operation Lafiya Dole, Clement Ayogu, ta hanyar umurnin Jami'in Tutar da ke Kula da Rundunar Sojojin Ruwa ta Gabas, Rear Adm Sanusi Ibrahim.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda da 'yan bindiga sun mamaye murabba'in mita 1,129 na gandun dajin Najeriya

'Yan sanda sun cafke 'yan fasa kwabri da mota makare da soyayyun kaji

A wani labarin, 'Yan sandan New Zealand sun kama wasu mutane biyu da ke kokarin shigo da mota da ke cike da soyayyun kaji zuwa Auckland, The Punch ta ruwaito.

Auckland, birni mafi girma a kasar, yana cikin tsauraran ka'idojin takunkumi na Korona tun tsakiyar watan Agusta, ba tare da an ba kowa izinin shiga ko barin yankin ba.

Duk kasuwancin da ba su da mahimmanci, wanda ya hada da wuraren cin abinci na kan titi, an rufe su a Auckland. Sai dai, sauran yankunan New Zealand na da karancin ka'idoji tare da kusan dukkanin nau'ikan kasuwanci a bude.

Asali: Legit.ng

Online view pixel