Da duminsa: Gwamnatin Dubai ta alanta neman yan Najeriya 6 ruwa a jallo, jerin sunayensu

Da duminsa: Gwamnatin Dubai ta alanta neman yan Najeriya 6 ruwa a jallo, jerin sunayensu

  • Akwai sunan yan Najeriya shida cikin jerin yan ta'addan da UAE ke nema
  • Sunayen sun nuna cewa akwai alamun dukkansu yan Arewa ne
  • Har yanzu, yan Najeriya ba sa iya zuwa kasar UAE tun bayan da kasar ta kakaba takunkumi

Hadaddiyar daular Larababawa UAE ta alanta neman wasu yan Najeriya shida kan laifin ta'addanci.

Yan Najeriyan na ckin jerin mutum 38 da kamfanoni 15 da gwamnatin UAE ta saka cikin jerin sunayen da ke da alaka da ta'addanci, cewar kafar yada labaran Al Arabiya.

A cewar rahoton:

"WAM ta bayyana cewa an yanke wannan shawara ne bisa yunkurin UAE na dakile mutane da kamfanonin dake daukar nauyin ta'addanci da kuma masu alaka da su."

Daga cikin mutane 38 da aka katabta, akwai yan kasar Lebanon 2, yan Yaman 2, yan Syriya biyar, yan Iran 5, yan Iraqi 2, sai kuma yan Indiya, Afghanistan, Britain, Saint Kitts-Navis, Russia, da Jordan .

Kara karanta wannan

Dalibin Jami'a ya yi garkuwa da dan'uwansa dan shekara biyar a jihar Katsina, ya shiga hannu

Da duminsa: Gwamnatin Dubai ta alanta neman yan Najeriya 6 ruwa a jallo, jerin sunayesu
Da duminsa: Gwamnatin Dubai ta alanta neman yan Najeriya 6 ruwa a jallo, jerin sunayesu Hoto: UAE
Asali: Getty Images

Ga jerin yan Najeriya shida da ake nema:

Abdurrahaman Ado Musa

Salihu Yusuf Adamu

Bashir Ali Yusuf

Muhammed Ibrahim Isa

Ibrahim Ali Alhassan

Surajo Abubakar Muhammad

Asali: Legit.ng

Online view pixel