Sace dalibai 73 a Zamfara: ACF ta dau zafi, ta ce duk gwamnatin da ba za ta kare al’umma ba bata da amfani

Sace dalibai 73 a Zamfara: ACF ta dau zafi, ta ce duk gwamnatin da ba za ta kare al’umma ba bata da amfani

  • Kungiyar Arewa Consultative Forum ta yi Allah wadai da sace dalibai guda 73 da wasu 'yan bindiga suka yi a jihar Zamfara
  • ACF ta bayyana cewa babu wani amfani a wanzuwar gwamnati da ba za ta iya kare al'ummanta ba
  • A ranar Laraba, 1 ga watan Satumba ne dai 'yan bindigar suka kai farmaki wata makaranta da ke karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara sannan suka yi awon gaba da dalibai da dama

Kaduna - Kungiyoyin Arewa Consultative Forum, da Southern Kaduna Peoples Union sun yi Allah wadai da sace dalibai 76 da wasu ‘yan bindiga suka yi a jihar Zamfara a jiya Laraba, 1 ga watan Satumba.

Sakataren yada labarai na kungiyar ACF, Emmanuel Yawe, ya bayyana bakin cikinsa kan sabon harin da sace daliban.

Kara karanta wannan

Tsohon gwamnan Neja: Dole ne a ilmantar da 'yan Najeriya idan ana son bindiganci ya kare

Sace dalibai 73 a Zamfara: ACF ta dau zafi, ta ce duk gwamnatin da ba za ta kare al’umma ba bata da amfani
Kungiyar ACF ta ce duk gwamnatin da ba za ta kare al’umma ba bata da amfani Hoto: Governor Bello Matawalle
Asali: Facebook

Kakakin na ACF ya shaida wa jaridar Punch a Kaduna, a ranar Laraba, cewa kungiyar ta arewacin kasar ba ta jin dadin ayyukan 'yan fashi da ke gudana a yankin.

Duk gwamnatin da ba za ta iya kare 'yan kasa ba ba ta da amfani - ACF

Yawe ya bayyana cewa duk gwamnatin da ba za ta iya kare 'yan kasarta ba toh lallai ba ta da wani amfani na wanzuwa.

Ya ce:

"To, wani mataki Matawalle ya dauka? Bai kamata mutane su yi sanarwa ba kawai. Idan yana kira ga jama'a su tashi su kare kansu, ya kamata ya iya yin kari a duk kokarin da jama'a ke yi."

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da dalibai da dama a wata makaranta a jihar Zamfara

Kara karanta wannan

Idan babu namijin da ya furta maki so, ki yi amfani da asiri, wata budurwa ta bayar da shawara a bidiyo

Da farko mun kawo cewa wasu ‘yan bindiga da ake zaton masu garkuwa da mutane ne sun kai farmaki wata makaranta da ke karamar hukumar Maradun a jihar Zamfara.

An tattaro cewa maharan sun kuma yi awon gaba da wasu dalibai da dama a makarantar wacce take ta maza da mata a hade.

Sashin Hausa na BBC ta ruwaito cewa mazauna garin Kayan Maradun sun sanar da ita cewa lamarin ya afku ne a safiyar ranar Laraba, 1 ga watan Satumba. Sun kuma bayyana cewa ba a san adadin daliban da maharan suka sace ba.

Hukumar yan sanda ta bayyana adadin daliban da aka sace a jihar Zamfara

Hakazalika hukumar yan sandan jihar Zamfara ta bayyana adadin daliban da aka sace a makarantar GDSS Kaya dake karamar hukumar Maradun ta jihar a ranar Laraba.

Kakakin hukumar yan sandan jihar, Muhammadu Shehu, a jawabin da ya saki yace yara 73 yan bindigan suka dauke, TVC ta ruwaito.

Kara karanta wannan

'Yan ta'adda sun kutsa gidan dan sanatan Kebbi a cikin gidansa, sun hallakashi

Asali: Legit.ng

Online view pixel