Alaka da Ta’addanci: Jerin Sarakuna 8 da Aka Dakatar Bisa Hada Kai Da ’Yan Bindiga

Alaka da Ta’addanci: Jerin Sarakuna 8 da Aka Dakatar Bisa Hada Kai Da ’Yan Bindiga

  • Jihohin Katsina da Zamfara suna ci gaba da fuskantar barazanar kashe-kashe da sace-sacen 'yan bindiga
  • Gwamnatoci sun dauki matakai don ganin an dakile munanan ayyukan 'yan ta'adda a yankunan Katsina da Zamfara
  • Daga cikin matakan, akwai dakatar da sarakunan gargajiya, wannan yasa muka tattaro jerin sarakunan da aka dakatar zuwa yanzu

Hare-haren 'yan bindiga na kara ta'azzara a yankin Arewa maso yammacin Najeriya, musamman jihar Zamfara, lamarin da ya kai asarar rayuka da dama da kuma dukiyoyin da suka zarce kimantawa.

Ana zargin wasu sarakunan gargajiya da hade kai da 'yan bindiga a yankunansu, wanda yana daya daga cikin matsalolin da suka kara yawaitar aikata muggan laifuka a wasu jihohin.

Gwamnatin jihar Zamfara ta sake dakatar da daya daga cikin manyan sarakunan jihar kan zargin alaka da 'yan bindiga, BBC ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Nasara: Tsageru sun sha ragargaza yayin da suka farmaki sansanin soji a jihar Neja

Basaraken shi ne na hudu cikin manyan sarakuna da gwamnatin Zamfara ta dakatar, akwai kuma wasu hakimai da gwamnati ta dakatar.

Sarkin ya nada wani shahrarren dan ta'adda, Ado Aleru, matsayin Sarkin Fulanin yankin.

Legit.ng Hausa ta tattaro rahotannin sarakuna da masu mukaman gargajiya da gwamnatin jihar ta dakatar.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

KU KARANTA: Me Ya Rage Nake Nema: Masari Ya Ce Daga 2023 Zai Yi Sallama da Siyasa

1. Sarkin Zurmi

Ta'addanci: Jerin sarakuna 7 da aka dakatar saboda hada kai da 'yan bindiga
Sarkin Zurmi, Atiku Abubakar | Hoto: bbc.com/hausa
Asali: UGC

Sarkin Zurmi, Atiku Abubakar shi ne basarake na baya bayan nan da gwamnatin jihar Zamfara ta dakatar kan zargin alaka da kashe-kashen da 'yan bindiga ke yi a yankin masarautarsa, PM News ta ruwaito.

Gwamnati ta tsige shi, sannan ta umarci Bunun Kanwa, Bello Suleiman, da ya karbi jagorancin masarautar nan take.

2. Sarkin Dansadau

Ta'addanci: Jerin sarakuna 7 da aka dakatar saboda hada kai da 'yan bindiga
Sarkin Dansadau, Hussaini Umar | Hoto: bbc.com/hausa
Asali: UGC

A ranar 1 ga watan Yuni gwamnan Zamfara Bello Matawalle ya dakatar da Sarkin Dansadau, Hussaini Umar kan zargin alaka da 'yan bindiga, in ji rahoton Nigerian Tribune.

Kara karanta wannan

Rundunar yan sanda ta ayyana neman shugaban yan bindiga, Ado Aleru, ruwa a jallo

Dagacin Dansadau Nasiru Muhammad Sarkin Kudu ya karɓi ragamar masarautar bayan dakatar da sarkin, kuma an kafa kwamitin bincike akansa.

3. Sarkin Maru

Ta'addanci: Jerin sarakuna 7 da aka dakatar saboda hada kai da 'yan bindiga
Sarkin Maru Abubakar Chika | Hoto: bbc.com/hausa
Asali: UGC

Rahoton Sun News ya ce, a watan Agustan 2019 gwamna Matawalle na Zamfara ya tsige Sarkin Maru Abubakar Chika bisa zargin cin amanar talakawansa ta hanyar kulla alaka da 'yan bindiga masu kashewa da satar mutane da dukiyoyi

Sai dai a nashi bangaren sarkin na Maru ya musanta zarge-zargen da ake yi masa.

4. Dagacin garin Kanoma

Dagacin garin Kanoma a karamar hukumar Maru ta jihar Zamfara, Alhaji Lawal Ahmad shi ma an dakatar da shi bisa zargin kulla alaka da masu sata da garkuwa da jama'a.

Gwamnatin Zamfara ta dakatar da shi ne tare da Sarkin Maru Abubakar Chika a shekarar 2019 bayan gano yadda 'yan bindiga ke amfani dasu wajen cutar da jama'a.

5. Dagacin Nasarawa Mailayi

An dakatar da Dagacin Nasarawa Mailayi, Bello Kiyawa, tare da sarkin Zurmi saboda zarginsu da kulla alaka da 'yan bindiga a cutar da jama'arsu.

Kara karanta wannan

Yanzu Yanzu: An tsige mataimakin gwamnan jihar Oyo daga kan kujerarsa

Gwamnati ta zargi hakimin da ya hada baki da 'yan bindiga masu addabar jihar, lamarin da ya kai ga tsige shi tare da maye gurbinsa da wani.

6. Sarkin Yakin Kanwa da Marafan Bakura

A watan Janairun 2020 gwamnatin ta dakatar da Alhaji Bello Garba Kanwa, Sarkin Yakin Kanwa da kuma Alhaji Muhammad Bello Yusuf wanda shi ne Marafan Bakura, rahoton Daily Trust ya kawo.

Gwamnatin Zamfara ta ce ta dakatar da sarakunan biyu ne bisa laifin raina gwamnati da kuma karan tsaye ga shirye-shiryenta, cin amanar al'umma da almundahana.

7. Sarkin Fawwa, Hakimin Kankara

Ta'addanci: Jerin sarakuna 7 da aka dakatar saboda hada kai da 'yan bindiga
Sarkin Fawwa, Hakimin Kankara, Alhaji Yusuf Lawal | Hoto: bbc.com/hausa
Asali: UGC

A watan Mayun 2021 aka dakatar da Sarkin Fawwa, Hakimin Kankara, Alhaji Yusuf Lawal, bisa zarginsa da ake yi masa na kulla alaka da 'yan bindiga da suka addabi jihar Katsina, in ji Daily Trust.

Masarautar Katsina ta ce ta dauki wannan mataki ne domin jaddada wa gwamnati da al'umma cewa tana goyon bayan yaki da ta'addanci da mahukunta ke yi.

Kara karanta wannan

Da duminsa: Gwamna ya dakatar da Sarkin da ya ba shaharren shugaban 'yan bindiga sarauta

Tuni aka kafa kwamitin bincike kan lamarin.

8. Sarkin Birnin Ƴandoto, Aliyu Marafa

Gwamna Jihar Zamfara Bello Matawalle ya dakatar da Sarkin Birnin Ƴandoto, Aliyu Marafa saboda naɗa shugaban yan bindiga da ake nema ruwa a jallo, Adamu Aliero-Yankuzo, Sarkin Fulani, rahoton Daily Trust.

Matakin da masarautar ta dauka na nada ɗan bindigan sarauta ya janyo cece-kuce inda da dama suka soki naɗin sarautar da aka yi wa ɓata garin.

Amma, cikin wata sanarwa da sakataren gwamnati, Kabiru Balarabe ya fitar, gwamnatin ta nesanta kanta daga matakin sarkin, ta kuma dakatar da sarkin sannan ta kafa kwamiti don bincike kan lamarin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel