Rashin Tsaro: An Shiga Rudani Yayinda Gwamnan APC Ya Caccaki INEC a Kan Sanar da Ranakun Zaben 2023
- An samu sabani tsakanin Gwamna David Umahi na jihar Ebonyi da INEC kan sanarwar ranakun zaben 2023
- Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, a ranar Laraba, 28 ga Afrilu ya sanar da ranakun zaben na 2023
- Sai dai kuma, Umahi ya caccaki hukumar zaben kan yin magana game da zaben ana tsaka da rashin tsaro a kasar
David Umahi, gwamnan jihar Ebonyi, a ranar Juma’a, 30 ga Afrilu, ya far wa Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), saboda sanar da ranakun da za a gudanar da babban zabe na 2023 ana tsaka da fama da matsalolin tsaro a kasar.
Shugaban hukumar INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya sanar da hakan a ranar Laraba, 28 ga watan Afrilu, yayin taron yini guda da aka gudanar don sauraron laifukan zabe na 2021 da kwamitin Majalisar Dattawa kan INEC ya shirya.
KU KARANTA KUMA: El-Rufai Yana Nema Wa Hukumomin Tsaro Kudi, Ya Koka Kan Karuwar Fashi da Makami

Asali: Facebook
Legit.ng ta tattaro cewa Umahi yayi magana ne yayin mika motocin da gwamnatin jihar ta sayo ga hukumomin tsaro da kuma Ebube-Agu, kayan tsaro na kudu maso gabas a masaukin gwamnan, Abakaliki.
Ya ce abin takaici ne yadda hukumar zaben ke magana kan zaben alhalin kasar tana cikin wani hali.
Umahi ya ce:
“Kasar tana fuskantar kalubale yanzu. Ba batun shugaban kasa ko gwamna bane. Wajibi ne dukkan shugabanni su ɗauki nauyi a wannan matakin saboda ba abin da kuke wa’azinsa a cikin jama’a ba ne yayin da muke tunkarar batun cewa dole mu kare makomar yaranmu. Me kuke yi da wannan? ”
Sai dai kuma, mai magana da yawun shugaban INEC, Rotimi Oyekanmi, ya ce ranar da za a gudanar da babban zaben na 2023 ya dogara ne da tsarin da INEC ta kafa tun a shekarar 2018.
KU KARANTA KUMA: Zan Yi Duk Me Yiwuwa Don Dawo da Zaman Lafiya da Tsaro a Najeriya – Buhari
Ya ce hukumar ta yanke shawarar hakan ne domin tabbatar da gaskiya, ya kara da cewa babban zaben a Najeriya zai dunga kasancewa a ranar Asabar ta uku ta Fabrairun shekarar zabe.
A wali labarin, yayin da gwamnatocin tarayya da na jihohi ke kokarin magance matsalar rashin tsaro a kasar, David Umahi, gwamnan jihar Ebonyi, ya bayyana cewa a shirye yake ya sasanta al'amura tare da 'yan fashi.
Da yake magana a ranar Juma’a, 30 ga Afrilu, a Abakiliki, Umahi wanda ya bayyana ‘yan fashin a matsayin “’ya’yanmu” ya ce yana son gano abin da ke damunsu don samar da mafita ga kalubalen tsaro da jihar ke fuskanta a yanzu.
Asali: Legit.ng