Shugaban Amurka Joe Biden na tattaunawa da Buhari da sauran shugabannin duniya

Shugaban Amurka Joe Biden na tattaunawa da Buhari da sauran shugabannin duniya

Shugaban Amurka, Joe Biden, ya gayyaci Muhammadu Buhari da sauran shugabannin duniya 39 zuwa taron koli kan canjin yanayi.

Fadar White House a cikin wata sanarwa ta bayyana cewa taron kwanaki biyu da za a fara ranar Alhamis, 22 ga Afrilu, an shirya shi ne da nufin jan hankalin kasashe don su kara kaimi wajen yaki da canjin yanayi kafin lokaci ya kure.

Har ila yau, manyan jami’ai, shugabannin kamfanoni, da manyan mutane a duniya kamar Paparoma Francis da mai taimakon jama'a, Bill Gates, wadanda aka shirya za su gabatar da jawabai, sun halarci taron.

Shugaban Amurka Joe Biden na tattaunawa da Buhari da sauran shugabannin duniya
Shugaban Amurka Joe Biden na tattaunawa da Buhari da sauran shugabannin duniya Hoto: The Asahi Shimbun, Femi Adesina/Facebook
Asali: UGC

KU KARANTA KUMA: Yan bindiga sun kashe basarake da wasu mutum uku a jihar Binuwai

Ga jerin sunayen shugabannin duniya da ke halartar taron:

1. Shugaba Muhammadu Buhari, Najeriya

2. Firayim Minista Gaston Browne, Antigua da Barbuda

3. Shugaba Alberto Fernandez, Ajantina

4. Firayim Minista Scott Morrison, Ostiraliya

5. Firayim Minista Sheikh Hasina, Bangladesh

6. Firayim Minista Lotay Tshering, Bhutan

7. Shugaba Jair Bolsonaro, Brazil

8. Firayim Minista Justin Trudeau, Kanada

9. Shugaba Sebastián Piñera, Chile

10. Shugaba Xi Jinping, Jamhuriyar Jama'ar Sin

11. Shugaba Iván Duque Márquez, Colombia

12. Shugaba Félix Tshisekedi, Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo

13. Firayim Minista Mette Frederiksen, Denmark

14. Shugaba Ursula von der Leyen, Hukumar Tarayyar Turai

15. Shugaba Charles Michel, Majalisar Turai

16. Shugaba Emmanuel Macron, Faransa

17. Shugaba Ali Bongo Ondimba, Gabon

18. Shugabar gwamnati Angela Merkel, Jamus

19. Firayim Minista Narendra Modi, Indiya

20. Shugaba Joko Widodo, Indonesia

21. Firayim Minista Benjamin Netanyahu, Isra'ila

22. Firayim Minista Mario Draghi, Italiya

23. Firayim Minista Andrew Holness, Jamaica

24. Firayim Minista Yoshihide Suga, Japan

25. Shugaba Uhuru Kenyatta, Kenya

26. Shugaba David Kabua, Jamhuriyar Tsibirin Marshall

27. Shugaba Andrés Manuel López Obrador, Mexico

28. Firayim Minista Jacinda Ardern, New Zealand

29 Firayim Minista Erna Solberg, Norway

30. Shugaba Andrzej Duda, Poland

31. Shugaba Moon Jae-in, Jamhuriyar Koriya

KU KARANTA KUMA: Hotuna da bidiyon kasaitaccen bikin mutuwar aure da wata yar Najeriya tayi

32. Shugaba Vladimir Putin, Tarayyar Rasha

33. Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud, Masarautar Saudi Arabiya

34. Firayim Minista Lee Hsien Loong, Singapore

35. Shugaba Matamela Cyril Ramaphosa, Afirka ta Kudu

36. Firayim Minista Pedro Sánchez, Spain

37. Shugaba Recep Tayyip Erdoğan, Turkiyya

38. Shugaba Sheikh Khalifa bin Zayed Al Nahyan, Hadaddiyar Daular Larabawa

39. Firayim Minista Boris Johnson, United Kingdom

40. Shugaba Nguyễn Phú Trɔng, Vietnam

A wani labarin, shugaba Muhammadu Buhari ya gana da kungiyar gwamnonin Arewacin Najeriya karkashin jagorancin gwamnan jihar Plateau, Simon Bako Lalong.

Mai magana da yawun shugaban kasa, Femi Adesina, ya ce anyi wannan zama ne ranar Alhamis a fadar shugaban kasa.

Daga cikin wadanda suka halarci zaman akwai gwamnan jihar Zamfara, Muhammad Bello Matawalle; gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal; da gwamnan jihar Kaduna, Nasir Ahmed El-Rufa'i.

Asali: Legit.ng

Online view pixel