Yawan kabilu da addinai ke jawo kalubale wajen gina Najeriya, Osinbajo

Yawan kabilu da addinai ke jawo kalubale wajen gina Najeriya, Osinbajo

- Mataimakin shugaban kasar Najeriya ya bayyana irin wahalar da ke cikin gina Najeriya

- A cewarsa, Najeriya wata irin kasa ce da gina zai zama da wuya saboda yawan kabilu

- Hakazalika ya yi kira ga 'yan Najeriya da su yi hakuri da juna domin kawo ci gaba ga kasar

Mataimakin Shugaban kasan Najeriya Yemi Osinbajo ya ce gina kasa mai kabilu daban-daban kamar Najeriya na iya zama da rudani da matukar wahala, TheCable ta ruwaito.

Wata sanarwa daga Laolu Akande, mai magana da yawun Osinbajo, ta nakalto shi yana cewa aikin gina kasar na iya zama kalubale duba da yawan kalubalantar juna ta fuskar dabi’u da hakurin ‘yan kasa daga sassa daban-daban.

Ya yi wannan magana ne a wani taro kan ci gaban kasa da jaridar Global Patriot tare da hadin gwiwar karamin ofishin jakadancin Najeriya da ke New York da kuma kungiyar 'Yan Najeriya mazauna kasashen waje (NIDO), reshen New Jersey suka shirya.

KU KARANTA: Zulum ya dira sansanin 'yan gudun hijira cikin dare, ya gano 'yan gudun hijiran bogi

Ba abu ne mai sauki ba gina kasa mai cike da kabilu irin Najeriya, Osinbajo
Ba abu ne mai sauki ba gina kasa mai cike da kabilu irin Najeriya, Osinbajo Hoto: The Punch Newspaper
Asali: UGC

Mataimakin shugaban kasar ya kara da cewa gina kasa "kalubale ne da aka jefa shi ga kowa, ya yi gini, ba ya rusawa" kuma "a tara, ba a kwashe ba."

"Aikin gina kasa yana aiki kuma har ma yana iya zama kamar rikici yayin da ake ci gaba, musamman a cikin kasa mai kabilu da addinai daban-daban kamar Najeriya," in ji shi.

“Yana kalubalantar dukkan dabi’u, hakuri da kuma hakuri da 'yan kasa; yana iya zama da wuya.”

Osinbajo ya kuma nanata kiran sa ga ‘yan sandan jihohi da su baiwa jihohi ikon magance matsalolin tsaron su.

“Dole ne mu yarda da cewa akwai bukatar kara rarraba karfin 'yan sanda. Na kasance mai yawan bayar da fatawa kan harkokin 'yan sanda na jihohi kuma na yi imanin haka lallai na iya zama dole kuma hanyar da za mu bi," aka ruwaito shi yana cewa

"Majalisar Dokoki ta Kasa na cikin wani matsayi na yin la’akari da wasu shawarwarin da suka je musu da nufin mika karin iko ga jihohi don ingantawa da kuma magance matsalolin tsaro.”

KU KARANTA: Fadar Shugaban Kasa: Buhari bai jikkata ba bayan yin rigakafin Korona

A wani labarin, Shugaba Muhammadu Buhari, Mataimakinsa Yemi Osinbajo, Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Boss Mustapha da sauran fitattun ‘yan Najeriya za su kasance cikin sahun farko na 'yan Najeriya da zasu yi allurar rigakafin COVID-19 ta gidan talabijin kai tsaye.

Ana sa ran za su fara allurar ta farko a ranar Asabar, 6 ga Maris.

Babban Darakta/Shugaba, na Hukumar Kula da Lafiya a Matakin Farko (NPHCDA), Dokta Faisal Shuaib, ya bayyana haka ne a ranar Litinin a taron hadin gwiwa na kasa da aka yi na Kwamitin Shugaban Kasa (PTF) kan COVID-19.

Salisu Ibrahim, mai rubutu a masana'antar Legit.ng Hausa da ya fara aiki a baya-bayan nan. Ya kware wajen kawo rahotanni na siyasa, kimiyya, al'adu da sauran lamurran yau da kullum.

Ya yi karatun diploma a fannin karantar da turanci a jami'ar Ahmadu Bello, ya kuma karantar na tsawon shekaru 7.

A halin yanzu yana zangon karshe na karatun digiri a fannin ilimin fasahar sadarwa a International Open University.

Ku bibiyi shafinsa na twitter a @therleez

Asali: Legit.ng

Online view pixel