Cikin Hotuna: Gwamnan Neja ya karbi fasinjojin da 'yan fashi suka saka

Cikin Hotuna: Gwamnan Neja ya karbi fasinjojin da 'yan fashi suka saka

- Gwamnan jihar Neja ya sanar da sake fasinjojin da aka sace a hanyar zuwa Minna

- A baya dai an sace fasinjojin ne kafin daga bisani aka sace wasu dalibai a Kagara

- A halin yanzu gwamnati ta karbi wadanda aka saka mutum 53 cikin koshin lafiya

Gwamnatin jihar Neja ta karbi faasinjoji 53 da aka sace makon da ya gabata a kan hanyarsu ta komawa garin Minna.

Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi
Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi Hoto: @chiefpressngs
Asali: Twitter

Gwamnatin jihar ta wallafa tabbacin sakin fasinjojin a shafinta na Twitter tare da nuna hotunan fasinjojin tare da gwamnan a cikin wani katafaren dakin taro.

KU KARANTA: Ku biya harajinku idan kuna son Abuja ta koma kamar Dubai, Hukumar Haraji

Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi
Hoto: @chiefpressngs
Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi
Asali: Twitter

Zuwa yanzu ana ci gaba da tsammanin sakin wasu dalibai da malamansu da aka sace a wata makarantar sakandare dake Kagara a jihar ta Neja.

Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi
Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi Hoto: @chiefpressngs
Asali: Twitter

Wani jita-jita nata yawo a kafafen sada zumunta cewa an saki daliban a jiya Lahadi. Sai dai gwamnan a tsakar daren jiya ya bayyana cewa zunzurun karya ce labarin cewa an sako daliban da malamansu.

KU KARANTA: Shugaba Buhari ya gargadi masu tada rikicin addini a jihar Gombe

Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi
Cikin Hotuna: Gwamnan jihar Neja ya karbi fasinjoji 53 da suka kubuta daga hannun 'yan fashi Hoto: @chiefpressngs
Asali: Twitter

A wani labarin, Da farko mun kawo muku cewa an sako mutane 42 da yan bindiga suka sace daga kwallejin kimiyya na gwamnati da ke Kagara a jihar Niger, bisa rahoton The Nation.

Wadanda aka sace sun hada da dalibai 27, ma'aikata 3 da kuma iyalan ma'aikatan su 12. Majiyoyi sun ce wadanda aka sace din suna kan hanyarsu na komawa Minna a yanzu.

Salisu Ibrahim, mai rubutu a masana'antar Legit.ng Hausa da ya fara aiki a baya-bayan nan. Ya kware wajen kawo rahotanni na siyasa, kimiyya, al'adu da sauran lamurran yau da kullum.

Ya yi karatun diploma a fannin karantar da turanci a jami'ar Ahmadu Bello, ya kuma karantar na tsawon shekaru 7.

A halin yanzu yana zangon karshe na karatun digiri a fannin ilimin fasahar sadarwa a International Open University.

Ku bibiyi shafinsa na twitter a @therleez

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.