'Yan fansho a jihar Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati

'Yan fansho a jihar Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati

- 'Yan fansho a jihar Gombe sun fito cincirindonsu don zanga-zanga kan rashin biyansu kudadensu

- Sun nemi haduwa da gwamnan jihar, sai da rahotanni sun bayyana baya gari a yayin zanga-zangar

- 'Yan fanshon sun samu ganawa da Sakataren gwamnatin jihar Fesfesa Ibrahim Njodi

Akalla mambobi dari uku na majalisar jihar Gombe na kungiyar 'yan fansho ta Najeriya a ranar Laraba suka toshe babbar kofar shiga gidan gwamnatin jihar ta Gombe lamarin da ya haifar da cunkoson ababen hawa a yankin, jaridar Punch ta ruwaito.

A cewar Mohammed Abubakar, shugaban karamar hukumar a tattaunawar da yayi da manema labarai, yan fanshon suna zanga-zangar rashin biyansu kudaden fansho da ya kwashe watanni.

KU KARANTA: Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya

'Yan fansho a Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati
'Yan fansho a Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati Hoto: The Punch
Asali: UGC

"Sauran korafe-korafen da 'yan fansho ke yi shi ne cewa sama da masu ritaya na kananan hukumomi 700 ba a sanya su a cikin fanshon na wata ba bayan sama da shekaru biyu na ritaya tsakanin wasu da dama," in ji Abubakar.

Ya tabbata, an ga jami’an tsaro a kofar gidan Gwamnatin suna ta fafutikar tabbatar da doka da oda yayin da masu zanga-zangar lumana suka dage kan ganin Gwamnan.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoton, majalisar ta ci gaba da ganawa da Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Njodi a madadin Gwamnan wanda rahotanni ke cewa baya cikin jihar.

KU KARANTA: 'Yan fasa kwabrin shinkafar waje sun jikkata wasu jami'an Kwastam da wani soja

'Yan fansho a Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati
'Yan fansho a Gombe sun yi zanga-zanga a gidan gwamnati Hoto: The Punch
Asali: UGC

A wani labarin, Gwamnan jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, ya nuna shirin gwamnatin jihar na kafa kwalejin addinin Musulunci da ke ba da difloma a kowace karamar hukuma 27 da ke fadin jihar.

Gwamnan ya bayyana shirin ne a jiya yayin bude taron jin ra’ayoyin jama’a na kwanaki uku kan cikakken gyaran tsarin koyar da ilimin addinin Musulunci na gargajiya, This Day ta ruwaito.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Salisu Ibrahim avatar

Salisu Ibrahim (Head of Hausa Desk) Salisu holds BSc in IT (IOU, 2021) and is AfricaCheck's ambassador. He brings over five years of experience in writing, publishing and management. Trained by prestigious newspapers like Reuters, AFP, and Solutions Journalism Network, he curates news stories for the Hausa-speaking audience. He rose from Hausa Editor to Head of Desk at Legit. His commitment to excellence has earned him recognition, including the 2021 Best Hausa Editor award and the Legit Fearless Team Player of the Year 2023.