Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya

Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya

- Gwamnatin jihar Abia ta bayyana cewa tana biyan fansar N100,000 a kan kowace saniya da aka kashewa makiyaya

- Gwamnatin ta bayyana hakan a matsayin wani yunkurin samar da zaman lafiya tsakanin makiyaya da manoma

- Gwamnan ya kuma bayyana cewa ana biyan su ma manoman N100,000 kan gonar da makiyaya suka shiga da shanu

Okezie Ikpeazu, gwamnan Abia, ya ce gwamnatin jihar na biyan makiyaya N100,000 kan kowace saniya da aka kashe sakamakon rikici tsakanin su da manoma, The Cable ta ruwaito.

Gwamnatin jihar a ranar Talata ta zargi makiyaya da sace ‘yan asalin jihar tare da lalata filayen noma tare da tura shanu cikin gonakai suna kiwo a bayyane.

Da yake magana a ranar Laraba a gidan talabijin na Channels Television na Sunrise Daily, Ikpeazu ya ce ana biyan irin wannan kudin ga manoma wadanda shanu suka bata gonakinsu.

Gwamnan ya ce an shirya wannan shiri ne domin samun amincewar mutane da kuma hana su daukar doka a hannunsu.

KU KARANTA: Wasu 'yan bindiga sun kashe wasu mazauna Kaduna a sabbin hare-hare

Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya
Abia: Muna biyan N100K kan duk wata saniya da aka kashewa makiyaya Hoto: The Whistler Ng
Asali: UGC

Da aka tambaye shi abin da gwamnatin jihar ke yi don tabbatar da doka kan hana kiwo a fili, Ikpeazu ya ce: “Muna da kakkarfan tsari wanda za mu yi amfani da shi wajen magance rikicin makiyaya na yau da kullun.

"Muna da abin da muke kira kwamitin magance rikicin manoma / makiyaya daga jihar inda CP yake shugabantar kananan hukumomi inda shugabannin zartarwa na kananan hukumomi ke shugabanta.

"Kuma mambobin kwamitin sun hada da Miyetti Allah, DSS da DPO na kananan hukumomi daban-daban har zuwa jihar.

"Kuma muna biyan diyyar kusan N100,000 ga duk wata saniya da aka kashe saboda rashin fahimtar juna tsakanin manoma da makiyayan kuma muna biyan irin wannan adadin don gonakin da aka tabbatar da cewa shanu da suka bata sun tattake ko sun lalata su."

Ikpeazu ya ce hanya mafi dacewa ta magance matsalar rikicin manoma da makiyaya shi ne gwamnatin tarayya ta magance tushen matsalar.

“Nijeriya ba ta bincikar matsalar yadda ya kamata. Matsalolin da muke fuskanta a kasar nan akwai su,” in ji shi.

'Yan asalin Biafra (IPOB) a ranar Talata sun ce kungiyar tsaro ta Gabas (ESN), reshenta na tsaro, za ta fara aiwatar da dokar hana kiwo a yankin kudu maso gabas.

IPOB ta bayar da wa’adin kwanaki 14 ga gwamnonin kudu maso gabas don tilasta dokar hana kiwo.

KU KARANTA: Kwalejin kimiyya da fasaha na Adamawa za ta fara karatun digiri, in ji Rector

A wani labarin, Gwamnatin Ogun a ranar Litinin ta karyata rahotannin da ke nuna cewa ta nemi taimakon Sunday Adeyemo, da aka fi sani da Sunday Igboho, don magance laifuka a jihar, Premium Times ta ruwaito.

Kwamishinan yada labarai da dabaru na jihar, Abdulwaheed Odusile, ya yi watsi da rahoton a cikin wata sanarwa da ya fitar a Abeokuta sa’o’i bayan Igboho ya isa jihar.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel