Kashi 73 na malaman makarantun gwamnati a Najeriya kwararru ne - UBEC

Kashi 73 na malaman makarantun gwamnati a Najeriya kwararru ne - UBEC

- Hukumar UBEC ta bayyana cewa Najeriya na cikin yanayin karancin kwararrun malamai

- Hukumar ta nuna kokarin da gwamnatin tarayya ke yi don habaka ilimi a kasar

- Kaso sama da 70 na malaman da ke karantarwa a makarantun gwamnati kwararru ne

Najeriya a halin yanzu tana da karancin malamai 277,537 a cewar rahoton binciken ma'aikata na kasa na shekarar 2018 kan Makarantun Ilimin na Gwamnati da Masu zaman kansu a Najeriya, The Punch ta ruwaito.

Binciken na ma'aikata wanda Hukumar Kula da Ilimin Farko ta Kasa ta nuna ya nuna cewa "yayin da 73% na wadanda ke koyarwa a makarantun gwamnati kwararrun malamai ne, kashi 53 cikin 100 na malamai a makarantu masu zaman kansu ne suka cancanci koyarwa."

Hukumar ta ce su ne wadanda suke da mafi karancin abin da ake bukata na takardar shedar kammala karatun Najeriya a bangaren ilimi da sama da haka.

KU KARANTA: Yanzu yanzu: Kotu ta bayar da belin Sowore a kan kudi Naira miliyan 20

Kashi 73 kadai ne na malaman makaranta cancanta - UBEC
Kashi 73 kadai ne na malaman makaranta cancanta - UBEC Hoto: The Guardian
Asali: UGC

Sakataren zartarwa na UBEC, Dr. Hamid Bobboyi, wanda ya fadi hakan a cikin wata sanarwa da Shugaban (Hulda da Jama'a), David Apeh, ya fitar a ranar Lahadi a Abuja, duk da haka, ya bayyana cewa akwai gyare-gyaren da ke gudanarwa don magance matsalolin.

Ya kuma jaddada cewa kashi 10 cikin 100 (N10bn) na dukkan adadin da aka karɓa daga Asusun tattara kuɗaɗe na UBEC an tsara su ne don haɓaka ƙwararrun malamai ta hanyar Hukumar Kula da Ilimin Farko ta Jiha.

Bobboyi ya ce, “Kashi 10 cikin 100 na dukkan kudin da aka karba daga Asusun Haɓaka Kudaden an keɓe shi ne don ci gaban ƙwararrun malamai ta hanyar SUBEB.

KU KARANTA: APC tayi tir da tarzomar Amurka, ta roki Trump da yayi koyi da Buhari

“Duk da haka, daya daga cikin manyan kalubalen shine samun kwararrun malamai da zasu koyar da yaran a kasar. Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya na kokarin magance ta. A yanzu, kowane mahaifi yana son ɗanshi yayi karatun likitanci, Sharia, Tattalin Arziki, Injiniya da sauransu.

“Dangane da rahoton NPA na shekarar 2018 a kan Makarantun Ilimin Firamare na Gwamnati da Masu zaman kansu a Najeriya, Najeriya na da karancin malamai 277, 537.

A wani labarin, Hukumar Jarrabawar Shiga Jami'a (JAMB) ta sanar da bude kofar daga cibiyoyi don daura sunayen wadanda aka zaba domin shiga 2020/2021.

Magatakardar hukumar, Farfesa Is-haq Oloyede ne ya sanar da hakan a Abuja a ranar Talata, 5 ga Janairu, jaridar The Nation ta ruwaito.

Kwamitin ya ce duk tsarin shigar dole ne ya bi ta cikin Tsarin Gudanarwa da Shiga Kasa (CAPS) don amincewa.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel