Shugaban Amurka, Trump ya sanya wa kasashen Afrika 15 sabbin takunkuman shiga kasar

Shugaban Amurka, Trump ya sanya wa kasashen Afrika 15 sabbin takunkuman shiga kasar

- Amurka ta kakaba wa wasu kasashen Afrika sabbin takunkumai na shiga kasarta

- A sabuwar dokar tafiye-tafiye na Shugaba Donald Trump, dole sai kasashen sun fara biyan dala 15 kafin amincewa su tafi kasar

- Sabuwar dokar za ta fara aiki ne daga ranar 24 ga watan Disamba

Shugaban kasar Amurka, Donald Trump, ya sanya wata sabuwar dokar tafiye-tafiye ga kasashen Afrika 15 inda za su biya dala 15,000 kafin su ziyarci kasar.

Wannan sabuwar doka da aka sanya za ta fara aiki ne a ranar 24 ga watan Disamba, sashin Hausa na BBC ta ruwaito.

A cewar ma’aikatar harkokin wajen kasar, wannan shiri na wa’adin watanni shida wanda zai shafi masu ziyartar Amurka da yan kasuwa zai zamo darasi ga masu zama bayan bizarsu ta kare.

Shugaban Amurka, Trump ya sanya wa kasashen Afrika 15 sabbin takunkuman shiga kasar
Shugaban Amurka, Trump ya sanya wa kasashen Afrika 15 sabbin takunkuman shiga kasar Hoto: Getty Images
Asali: Getty Images

KU KARANTA KUMA: Majalisar dokokin Ondo ta tsige mataimakin kakakinta Iroju Ogundeji

Trump, wanda ya sha kaye a zaben kasar da aka gudanar, ya mayar da tsaurara matakai na shige da fice abu mai matukar muhimmanci a lokacin wa'adin mulkinsa na shekara hudu.

Zababben shugaban Amurka mai jiran gado, Joe Biden ya dau alkawarin sauya wasu matakan da Trump ya dauka musamman kan shige da ficen kasar.

Sabon tsarin bizar zai shafi kasashen da kashi 10 cikin 100 na al’ummansu da ke zuwa Amurka su wuce iya lokacin da aka ba su na zama a shekarar 2019, kuma a yanzu za a nemi su biya wasu kudade kimanin dala 5,000 da dala 10,000 ko kuma dala 15,000.

Sai dai a yayin da yan wadannan kasashe ke wuce lokacin zamansu a Amurka, masu zuwa daga kasashen ba su da yawa, kamar yadda Reuters ya ruwaito.

KU KARANTA KUMA: Hariji kuma matsafi: Kotu ta raba auren mijin da ke saduwa da matarsa tsawon awanni

Kasashen da matakin ya shafa sun hada da:

1. Angola

2. Burkina Faso

3. Chadi

4. Jamhuriyyar Dimokuradiyyar Congo

5. Djibouti

6. Eritrea

7. Gambia

8. Guinea-Bissau

9. Liberia

10. Mauritania

11. Sudan

12. Sao Tome

13. Cape Verde

14. Libya

15. Burundi

A wani labarin, mun ji cewa tohuwar ministar Birtaniya, Theresa Villiers ta yi kira ga gwamnatin Ingila ta maka takunkumi a kan jami’an gwamnatin tarayyar Najeriya.

Theresa Villiers ta na so a hukunta gwamnatin Najeriyan ne a game da yadda ta dauki matakai masu tsauri a kan masu zanga-zangar lumana.

Villiers ta ce bayanan da ta samu daga 'yan mazabarta wanda asalin ‘yan Najeriya ne ya nuna cewa an ci zarafin ‘yan zanga-zangar #EndSARS.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng