Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau

Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 216 a fadin Najeriya.

Kwana takwas a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbon wadanda suka kamu da cutar.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Laraba 2 ga Satumba, shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 216 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Plateau-59

Rivers-27

Abia-22

Lagos-20

Oyo-18

Enugu-17

Kaduna-11

FCT-11

Ogun-10

Ebonyi-4

Osun-4

Ekiti-4

Delta-3

Edo-3

Akwa Ibom-2

Bauchi-1

Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau
Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng