Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau

Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau

Hukumar Dakile Yaduwar Cututtuka ta Najeriya wato NCDC ta bayyana cewa annobar cutar Covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 216 a fadin Najeriya.

Kwana takwas a jere yanzu jihar Plateau na zarce Legas da Abuja wajen yawan adadin sabbon wadanda suka kamu da cutar.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da hukumar NCDC ta fitar da misalin karfe 11:na daren ranar Laraba 2 ga Satumba, shekarar 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na Twitter, ta sanar da cewa an samu karin sabbin mutane 216 da suka fito daga jihohin Najeriya kamar haka:

Plateau-59

Rivers-27

Abia-22

Lagos-20

Oyo-18

Enugu-17

Kaduna-11

FCT-11

Ogun-10

Ebonyi-4

Osun-4

Ekiti-4

Delta-3

Edo-3

Akwa Ibom-2

Bauchi-1

Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau
Da dumi-dumi: Sabbin yan Najeriya 216 sun kamu da cutar Korona yau
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Online view pixel