Majalisar wakilai ta gimtse hutun da ta tafi bayan barkewar annobar covid-19

Majalisar wakilai ta gimtse hutun da ta tafi bayan barkewar annobar covid-19

Majalisar waikilai ta tsayar da ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, 2020, a matsayin ranar da zata dawo daga hutun da ta tafi.

Jaridar 'OderPaperNG' ta rawaito cewa ta ga sakonnin sanarwa da aka aikewa mambobin majalisar da yammacin ranar Lahadi.

A cikin sakon sanarwar, mai dauke da sa hannun Patrick A. Giwa, magatakardar majalisa, an shawarci sauran hadiman mambobin majalisa su cigaba da zama a gida zuwa sanarwa ta gaba.

A cewar sanarwar, "za a yi zaman majalisar ne bisa biyayya ga shawarwarin hukumar NCDC da kuma wasu sabbin matakai da majalisa ta dauka."

Sanarwar ta bayyana cewa; "mu na sanar da dukkan mambobin majalisar wakilai cewa za a dawo zaman majalisa a ranar Talata, 28 ga watan Afrilu, da misalin karfe 10:00 na safe.

Majalisar wakilai ta gimtse hutun da ta tafi bayan barkewar annobar covid-19
Majalisar wakilai ta gimtse hutun da ta tafi bayan barkewar annobar covid-19
Asali: UGC

"Ana shawartar mambobi a kan su kiyaye da sabon lokacin da aka bayyana a matsayin ranar dawowa daga hutun.

"Za a gudanar da zaman majalisa bisa kiyaye matakan da hukumar NCDC ta shimfida da kuma wasu karin matakai da majalisa ta dauka, wanda za a aika wa kowanne mamba.

DUBA WANNAN: Magoya bayan Buhari sun bayyana wanda su ke so ya maye gurbin marigayi Abba Kyari

"Ana shawartar sauran ragowar hadiman mambobin majalisa a kan su cigaba da aiki daga gida matukar ba neman mutum aka yi har zuwa fitowar sanarwa ta gaba."

A ranar 24 ga watan Maris ne majalisar wakilai ta tafi hutu sakamakon barkewar annobar covid-19.

Ana ganin cewa akwai harkokin da suka shafi annobar covid-19, musamman batun kudaden tallafi, da ake bukatar amincewar majalisa a kan yadda za a yi amfani da su.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng