Jerin kasashen Afirka da suka fi yawan masu cutar Korona – WHO

Jerin kasashen Afirka da suka fi yawan masu cutar Korona – WHO

- Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce an samu mutum fiye da 21,000 da suka kamu da Coronavirus a nahiyar Afirka

- Hukumar ta ce mutum 5,000 sun warke yayin da 1,000 sun mutu sakamakon annobar

- Rahoton da WHO ta wallafa ya nuna cewa mutum 3,158 sun kamu a Afirka ta Kudu, 2,629 a Algeria, 1,042 a Ghana sai 1,016 a Kamaru

Sama da mutane 21,000 aka ruwaito sun kamu da coronavirus a nahiyar Afirka, 5,000 sun warke yayin da 1,000 sun mutu a cewar Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO.

Hukumar ta wallafa kididigan yadda mummunar cutar ta yadu a mahiyar Afirka da adadin wanda cutar ta kashe zuwa ranar 2 ga watan Afrilu kamar yadda Legit.ng ta ruwaito.

A jerin kasashen da ta wallafa, WHO ta nuna cewa an samu mutum 541 da suka kamu da cutar a Najeriya wanda hakan ke nuna cewa an wallafa rahoton ne kafin hukumar NCDC ta Najeriya ta fitar da sabbin alkallumanta.

DUBA WANNAN: An kama mutumin da ya haike wa matarsa har ta mutu a Jigawa

Rahoto game da yaduwar cutar da NCDC ta fitar a daren ranar Asabar 24 ga watan Afrilu da karfe 11.3O ya nuna cewa mutum 1O95 ne suka kamu da cutar a kasar.

Mutum 2O8 sun warke an sallame su yayin da mutum 32 cutar da kashe tun bullar ta a kasar.

Rahoton da WHO ta wallafa ya nuna cewa mutum 3,158 sun kamu a Afirka ta Kudu, 2,629 a Algeria, 1,042 a Ghana sai 1,016 a Kamaru.

Ga dai sabon kididdigar yadda cutar ta yadu a kasashen nahiyar Afirka a kasa zuwa ranar 24 ga watan Afrilu.

Jerin kasashen Afirka da suka fi yawan masu cutar Korona – WHO
Jerin kasashen Afirka da suka fi yawan masu cutar Korona – WHO. Mallakin Hoto - WHO
Asali: Twitter

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164