Jerin sunayen 'yan majalisar Sarkin Karaye da ya rantsar
Sarkin Karaye Alhaji Ibrahim Abubakar II a ranar Litinin ya rantsar da kwamitin majalisar masarautarsa kuma sun yi taron farko a fadar Sarkina. Rantsarwar ta samu halarta shuwagabannin kananan hukumomi da kuma wasu manyan masu sarauta a masarautar ta Karaye.
Wannan na kunshe ne a takardar da jami’in yada labarai na masarautar Karaye, Haruna Gunduwawa ya fitar tare da mikata ga jaridar solacebase a ranar Litinin.
Idan zamu tuna dai, Gwamna Ganduje na jihar Kano ya samu nasarar tabbatar da dokar karin masarautu hudu a jihar bayan da majalisar jihar ta amince a ranar Alhamis.
Takardar tace, Sarkin Karaye wanda shine shugaban majalisar masarautarsa, ya mika godiyarsa ga gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje da ya sa hannu a kan dokar kirkirar sabbin masarautun a jihar.
DUBA WANNAN: FIRS: Fowler ya gode wa Buhari, ya 'sace' gwuiwar masu cewa an cire shi
Basaraken, kamar yadda takardar ta sanar, ya jinjinawa gwamnatin jihar da majalisar jihar a kan abinda ya kwatanta da babban kokari wajen tabbatar da sun cika bukatar mutanen jihar.
A taron, wanda aka tattauna lamurran tsaron masarautar, an bukaci hakimai da dagatai da su samarwa masu unguwanni rijistar da zasu dinga daukar sunan duk wani bako da ya shigo yankin masarautar.
“A matsayin hanyar tabbatar da zaman lafiya, tsaro da lumana a yankin masarautar, majalisar ta jaddada cewa akwai bukatar ‘yan kasuwa, shuwagabanni addinai da sauran masu ruwa da tsaki a yankin da su saka hannu wajen tabbatar da tsaron masarautar da jihar baki daya,” in ji takardar.
Taron ya amince da Alhaji Tijjani Usman Getso a matsayin sakatare masarautar. Sauran mambobin majalisar masarautar karayen sun hada da: Alhaji Isma’ila Gwarzo, Alhaji Jibrin Ibrahim Zarewa, Alhaji Lawan Sule Garo, Barista Balarabe Bello Rogo, Alhaji Sidi Mustapha Karaye da Alhaji Wada Na Kofar Yamma.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:
https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng