Harin Sokoto: Rundunar soji sun fara aiki na musamman

Harin Sokoto: Rundunar soji sun fara aiki na musamman

Rundunar sojin Najeriya sun kaddamar da wani aikin tsaro na hadin gwiwa domin kakkabe yan ta’adda masu fashi a kauyukan Gandi da Tabanni dake karamar hukumar Rabbah na jihar Sokoto.

A wata sanarwa da aka gabatar ga kamfanin dillancin labaran Naeriya a ranar Juma’a a Sokoto dauke da sa hannun kakakin sashi na 1, na rundunar sojin Sokoto, Clement Abiade, yace wannan aiki ya biyo bayan harin da yan fashin suka gudanar a ranar 9 ga watan Yuli wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Harin Sokoto: Rundunar soji sun fara aiki na musamman
Harin Sokoto: Rundunar soji sun fara aiki na musamman

Aikin ya hada da rundunar soji, sojin sama, yan sanda, NSCDC da kuma DSS sun fara a ranar Alhamis sannan kuma hakan zai kai har Zamfara.

KU KARANTA KUMA: Abunda muka tattauna da shugaba Buhari – Yan majalisa na APC

Kwamandan sashin, Kennedy Udeagbala, ya fadama dakarun das u tabbatar da an aiwaatar da aikin cikin hadin kai, da kuma kwarewa.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel