Najeriya tana cikin jerin Kasashen da su ka hadarin zama ga mata

Najeriya tana cikin jerin Kasashen da su ka hadarin zama ga mata

Mun samu labari cewa wani bincike da aka yi a Kasar waje ya nuna cewa akwai Kasar Najeriya cikin jerin Kasashen da su ke da hadarin zama matuka ga mata a duk fadin Duniya. Thomson Reuter’s ne yayi wannan bincike.

Najeriya tana cikin jerin Kasashen da su ka hadarin zama ga mata
Bincike ya nuna cewa zama a Najeriya akwai hadari ga mata

Najeriya dai ta samu shiga cikin sahun farko na kasashen da ke da hadarin zama ga mata a shekarar nan ta 2018 da ake ciki. Kasar da ta zo kan gaba a wannan jeri dai ita ce Indiya inda ake samun yawan fyade na ‘Ya ‘ya mata.

Bayan Kasar Indiya sai irin su Siriya da Somaliya da Fakistan da ma Afghanistan. A wadannan kasashen dai Musulmai su ne akasari. A cikin kasashen da aka jero dai har da Kasar Saudi Arabia inda yanzu mata ke samun sakewa.

KU KARANTA: Wasu mutane 10 sun mutu a hanyar Kano ta hadarin mota

Kasar Amurka da ice ta zo ta 10 a binciken da aka gudunar. Amurka ce Kasar da ba ta cikin Nahiyar Asiya da kuma Afrika da ta shiga cikin jerin.

Kasashen dai su ne:

1. Indiya

2. Afghanistan

3. Siriya

4. Somaliya

5. Saudi Arabia

6. Fakistan

7. Kongo

8. Yemen

9. Najeriya

10. Amurka

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel