Kishin-Kishin: Jam'iyyar adawa ta PDP na zawarcin Sanata Shehu Sani

Kishin-Kishin: Jam'iyyar adawa ta PDP na zawarcin Sanata Shehu Sani

Rahotannin da muke samu daga majiyoyin mu da dama na nuni ne da cewa jam'iyyar adawa ta Peoples Democratic Party, PDP a takaice na cigaba da zawarcin Sanata Shehu Sani da ke wakiltar mazabar jihar Kaduna ta tsakiya ya dawo cikin ta.

Mun samu kuma dai cewa Sanatan na ta fuskantar matsin lamba daga bangarori da dama kuma mabanbanta da suka hada da kungiyoyin matasa da ma dattijai daga jam'iyyar ta PDP.

Kishin-Kishin: Jam'iyyar adawa ta PDP na zawarcin Sanata Shehu Sani
Kishin-Kishin: Jam'iyyar adawa ta PDP na zawarcin Sanata Shehu Sani

KU KARANTA: Masu takarar shugabancin kasa sun kara yawa

Legit.ng ta samu haka zalika cewa yanzu haka ma dai wata kungiyar matasa ta jam'iyyar PDP din a mataki na tarayya ta PDP National Youth League ta fitar da sanarwa dauke da sa hannun shugaban ta Honourable Inioribo Tamunotonye da kuma jami'ar hulda da jama'a ta kungiyar Zainab Al-Amin suna rokon sa ya bar APC din.

A wani labarin kuma, Wata babbar kotu dake a unguwar Maitama a garin Abuja, babban birnin tarayya ta bayar da umurmi ga jami'an tsaron Najeriya da suka hada da 'yan sanda da kuma jami'an tsaron farin kaya watau SSS da kar su kuskura su kama Satana Ovie Omo-Agege daga jihar Delta.

Wannan dai kamar yadda muka samu ya biyo bayan bukatar Lauyan Sanatan mai suna Aliyu Umar ya roki kotun a cikin karar da ya shigar a gaban ta .

Idan ka na da wani shawara ko bukatan bamu labari, tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

KU LATSA: Sabuwar hanyar karanta labarain Legit.ng HAUSA

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel