Super Eagles Ta Shiga Jimami, Fitaccen Ɗan Kwallon Najeriya Ya Rasa Mahaifiyarsa

Super Eagles Ta Shiga Jimami, Fitaccen Ɗan Kwallon Najeriya Ya Rasa Mahaifiyarsa

  • Dan wasan Super Eagles Samuel Chukwueze ya rasa mahaifiyarsa Sarah Chukwueze a safiyar Alhamis bayan ta yi fama da rashin lafiya
  • An ce Chukwueze ya ci gaba da buga wasanni a kungiyar Fulham da Super Eagles cikin jajircewa duk da cewa lokacin mahaifiyarsa tana jinya
  • Hukumar kwallon kafa ta NFF ta nuna alhini kan wannan rashi dake zuwa kwanaki kadan bayan mutuwar mahaifin dan wasa Wilfred Ndidi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Tauraron ɗan wasan gaba na ƙungiyar Super Eagles, Samuel Chukwueze, ya shiga tsananin jimami na rashin mahaifiyarsa, Sarah Chukwueze, wadda ta rasu bayan fama da jinya.

Wannan babban rashi ya faru ne a safiyar ranar Alhamis, 29 ga Janairu, 2026, kamar yadda ɗan uwan ɗan wasan, David, ya sanar a shafinsa na sada zumunta.

Kara karanta wannan

Matashin da ya mallaki bindiga a Kano ya yi wa mahaifiyarsa dukan tsiya

Mahaifiyar dan wasan Najeriya, Samuel Chukwueze ta mutu
Samuel Chukwueze, dan wasan gaban Super Eagles da mahaifiyarsa ta rasu. Hoto: @NGSuperEagles
Source: Getty Images

Jinyar mahaifiyar ɗan wasan Super Eagles

Rasuwar Mrs. Chukwueze ta zo ne a daidai lokacin da masana'antar ƙwallon ƙafa a Najeriya ke jimamin rasuwar mahaifin kyaftin ɗin Super Eagles, Wilfred Ndidi, in ji rahoton Daily Trust.

Bincike ya nuna cewa Samuel Chukwueze ya daɗe yana gudanar da wasanninsa a ƙungiyar Fulham da Super Eagles cikin damuwa, amma bai bari duniya ta sani ba.

Majiyoyi na kusa da ɗan wasan sun bayyana cewa ya zaɓi ya ci gaba da yin horo da buga wasanni domin sauke nauyin da ke kansa, duk da cewa mahaifiyarsa tana jinya mai tsanani.

Wannan jajircewa tasa ta janyo masa yabo daga masoya ƙwallon ƙafa, waɗanda suka bayyana shi a matsayin gwarzo mai haƙuri da kishin ƙasa da ƙungiyarsa.

Hukumar NFF da NSC sun mika ta'aziya

Hukumar ƙwallon ƙafa ta Najeriya (NFF) ta nuna alhininta, inda ta bayyana marigayiyar a matsayin mace mai kyakkyawan tasiri a rayuwar ɗan wasan.

Kara karanta wannan

Tsautsayi: Mummunan hadari ya rutsa da mahaifin kyaftin din Najeriya har ya rasu

Sakataren NFF, Mohammed Sanusi, ya ce:

"Mun san yadda Mrs. Sarah Chukwueze ta kasance ginshiƙi ga yaranta. Muna addu'ar Allah Ya ba Samuel da sauran yan uwansa haƙurin jure wannan rashi."

Hukumar wasanni ta ƙasa (NSC) ma ta fitar da nata sakon ta'aziyyar, tana mai bayyana cewa daukacin masoyan wasanni a Najeriya suna tare da Chukwueze a wannan lokaci.

Hukumar kwallon kafar Najeriya (NFF) ta yi ta'aziyyar mahaifiyar Chukwueze
Tambarin hukumar kwallon kafar Najeriya, wacce aka kafa a 1945. Hoto: @thenff
Source: Getty Images

Jimami a sansanin Super Eagles

Mutuwar mahaifiyar Chukwueze ta ƙara jefa sansanin Super Eagles cikin makoki, mako guda kacal bayan rasuwar mahaifin Wilfred Ndidi a hatsarin mota.

A halin yanzu, saƙonnin jajantawa suna ta kwarara daga abokan wasansa na ƙungiyar Fulham, inda yake zaman aro daga AC Milan, da kuma sauran ƴan wasan duniya.

Daukacin al'ummar ƙwallon ƙafa suna kiran a haɗa kai wajen yi wa iyalan marigayiyar addu'a domin samun sauƙin wannan raɗadi da suke ciki, in ji rahoton Premium Times.

Mahaifin Kyaftin din Super Eagles ya mutu

Tun da faru, mun ruwaito cewa, Kyaftin din kungiyar kwallon kafa ta Najeriya watau Super Eagles, Wilfred Ndidi, ya rasa mahaifinsa, Sunday Ndidi.

Kara karanta wannan

Bayan 'dan Kwankwaso, wasu karin kwamishinoni sun fice daga gwamnatin Abba

Rahotanni sun bayyana cewa mahaifin nasa, wanda tsohon jami'in soja ne, ya rasu sakamakon hadarin mota mai muni da ya faru a ranar Talata a jihar Delta.

Kungiyar kwallon kafa ta Besiktas da ke kasar Turkiyya, wadda Ndidi ke bugawa wasa, ita ce ta sanar da wannan mummunan labari a wata sanarwa da ta fitar.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com