AFCON 2025: Gwamnatin Tarayya Ta Aika Sako ga Super Eagles yayin da Take Shirin Fafatawa da Morocco

AFCON 2025: Gwamnatin Tarayya Ta Aika Sako ga Super Eagles yayin da Take Shirin Fafatawa da Morocco

  • Tawagar Super Eagles ta Najeriya na shirin fafatawa da Atlas Lions na Morocco a wasan na kusa da na karshe a gasar cin kofin Nahiyar Afrika
  • Gwamnatin tarayya ta aika da sako mai muhimmanci yayin da 'yan wasan Super Eagles ke shirye-shiryen buga wasan na AFCON a yau
  • Za a buga wasan ne dai a ranar Laraba, 14 ga watan Janairun 2026 a birnin Rabat na Morocco da misalin karfe 9:00 na dare a agogon Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

FCT Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi muhimmin kira ga ’yan wasan Super Eagles yayin da suke shirin fafatawa da kasar Morocco a gasar AFCON 2025.

Gwamnatin tarayya ta bukaci 'yan wasan Super Eagles da su buga wasan cikin kwarin gwiwa da haɗin kai a wasan na kusa da na karshe na gasar cin kofin nahiyar Afrika (AFCON).

Kara karanta wannan

AFCON2025: Mourinho ya hango kasar da za ta yi nasara a wasan Najeriya da Moroko

Gwamnatin tarayya ta yaba da kwazon Super Eagles
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da 'yan wasan Super Eagles Hoto: @DOlusegun, @NGSuperEagles
Source: UGC

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa Ministan yaɗa labarai da wayar da kan jama’a, Mohammed Idris, ya fitar ranar Laraba, 14 ga watan Janairun 2026 a shafinsa na X.

Me gwamnati ta gayawa Super Eagles?

Miniatan ya ce daukacin ’yan Najeriya suna tare da tawagar baki ɗaya, inda ya yaba da ladabinsu, jarumtarsu da kuma irin amincewar da suka nuna tun farkon gasar.

“Yayin da kuke shirin fuskantar Morocco a wasan kusa da na karshe na AFCON, ina so ku sani cewa daukacin Najeriya tana nuna goyon baya a gare ku."

- Mohammed Idris

Ya ce irin bajintar da tawagar ta nuna zuwa yanzu ta sake tunatar da ’yan Najeriya dalilin da ya sa Super Eagles ke ci gaba da kasancewa ɗaya daga cikin kungiyoyin da aka fi girmamawa a nahiyar Afrika.

“Kun taɓa zuwa wannan mataki a baya; kun san abin da ake buƙata domin cin nasara a wannan matakin."

Kara karanta wannan

Jigon ADC ya zargi Tinubu da sakaci, an tsunduma mutane miliyan 141 a bakin talauci

- Mohammed Idris

An yaba da kwazon 'yan Super Eagles

Ministan ya ce nasarorin da Najeriya ta samu a gasar AFCON a baya da kuma cin galaba kan manyan abokan hamayya sun samo asali ne daga aiki tare, kwarin gwiwa da kuma zuciyar gwagwarmaya.

“Waɗannan nasarori ba sa’a ba ne; sun samo asali ne daga haɗin kai, kwarin gwiwa da zuciyar gwagwarmaya, kuma kun nuna irin wannan zuciyar a wannan gasar."

- Mohammed Idris

'Yan Najeriya na goyon-bayan Super Eagles

Mohammed Idris ya kara da cewa ’yan wasan na ɗauke da burin miliyoyin ’yan Najeriya yayin da suke shiga fili domin buga wasa.

“Yayin da ku ke taka leda a fili, ku tuna ba ku kaɗai ba ne; kuna ɗauke da burin miliyoyin ’yan Najeriya."

- Mohammed Idris

Gwamnatn tarayya ta ba 'yan kwallo shawara

Ya shawarci tawagar da su buga wasan cikin kwarin gwiwar zakaru (da kuma haɗin kan ’yan’uwantaka, tare da ci gaba da nuna kishirwar samun nasara.

Kara karanta wannan

AFCON 2025: Kocin Morocco ya fadi sunayen 'yan wasan Najeriya 3 da yake tsoro

“Ku ci gaba da mai da hankali, ku amince da juna, ku kuma ba da iyakar kokarinku daga busar farko har zuwa ta ƙarshe."

- Mohammed Idris

Gwamnatin tarayya ta karfafa gwiwar Super Eagles
Ministan yada labarai da wayar da kan jama'a, Mohammed Idris Hoto: @HMMohammedIdris
Source: Twitter

Ya ce ’yan wasan sun cancanci kaiwa matakin wasan kusa da na karshe, kuma suna da kwarewar da za ta kai su gaba a gasar.

“A yau da daddare, ku fita ku rubuta wani sabon babi na alfahari a tarihin kwallon ƙafa na ƙasarmu."
“Ku buga da zuciya, ku buga da alfahari, ku buga wa Najeriya.”

- Mohammed Idris

Super Eagles za su kara da Morocco ne a filin wasa na Prince Moulay Abdellah da ke Rabat, ranar Laraba da misalin karfe 9:00 na dare agogon Najeriya.

An yi wa Super Eagles tanadin kyauta

A wani labarin kuma, kun ji cewa hamshakin attajiri, Abdulsamad Rabiu BUA ya yaba da nasarar da Najeriya ta samu kan Algeria a gasar AFCON 2025.

Babban mai kudin ya ce zai ba da $100,000 ga kowace kwallon da aka ci a wasan kusa da na karshe da kasar za ta buga da Morocco.

Hakazalika, hamshakin attajirin ya yi alkawarin ba da makudan daloli idan har 'yan wasan Super Eagles suka samu nasara a wasan karshe.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng