Dembele Ya Kafa Tarihi bayan Doke Yamal a Kyautar Ballon d'Or 2025

Dembele Ya Kafa Tarihi bayan Doke Yamal a Kyautar Ballon d'Or 2025

  • Ousmane Dembele ya lashe kyautar zakaran dan kwallon duniya na maza watau Ballon d'Or 2025 a karon farko a tarihinsa
  • 'Dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta PSG ya samu wannan nasara ne bayan doke matashin dan Barcelona, Lamine Yamal
  • Dembele ya samu nasararo da dama a kakar wasan da ta gabata sakamakon bajintar zura kwallo, taimakawa da sauransu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da ƙkullum

France - Ɗan wasan gaba na kungiyar Paris Saint-Germain (PSG), Ousmane Dembele, ya lashe kyautar Ballon d’Or a karon farko a tarihi.

Fitaccen dan wasan ya lashe wannan kyauta ta Ballon d'Or, watau zakaran dan wasan da ya fi kowane kokari a maza a kakar wasan da ta gabata.

Ousmane Dembele.
Hoton dan wasan PSG, Ousmane Dembeledauke da kyautar Ballon d'Or Hoto: Fabrizio Romano
Source: Getty Images

Fabrizio Romano, fitaccen dan jarida mai kawo rahotanni kwallon kafa ne ya tabbatar da hakan a shafinsa na Facebook a daren yau Litinin.

Kara karanta wannan

Fitaccen Jarumin Fim ya sa jam'iyyu a ma'auni, ya gano wacce za ta kayar da Tinubu a 2027

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Nasarorin Dembele a kakar wasan 2024/2025

'Dan wasan mai shekara 28 ya zura kwallaye 35 tare da taimaka wajen cin kwallaye 16 a wasa 53 a kakar da ta gabata.

Dembele ya taimakawa kungiyar PSG ta lashe manyan kofuna uku ciki har da gasar zakarun nahiyar turai watau Champions League karo na farko a tarihin kulob din.

Tauraron dan wasan, dan asalin kasar Faransan ya kuma zama ɗaya daga cikin wadanda suka fi jefa kwallaye a raga a Ligue 1, inda ya ci kwallaye 21.

Sannan an zaɓe shi a matsayin zakakurin dan wasan shekara a gasar Ligue 1 ta Faransa, kuma aka ba shi kyautar gwarzon 'dan wasan zakarun Turai.

Yadda Dembele ya zama zakaran 2025

Dembele ya doke matashin ɗan wasan Barcelona mai shekara 18, Lamine Yamal, wanda ya zo na biyu tare da lashe Kopa Trophy, kyautar zakaran matashin dan kwallon da ya fi nuna bajinta.

Kara karanta wannan

Katsina: Kananan hukumomi 2 sun zauna da ƴan ta'adda ɗauke da mugayen makamai

'Dan wasan PSG, Vitinha, ya zo na uku, yayin da dan wasan gaba na kungiyar Liverpool ta kasar Ingila, Mohamed Salah, ya zo na hudu.

Cole Palmer na Chelsea ya zo na takwas. A bana Rodri na Manchester City bai shiga jerin sunayen ba sakamakon jinya a kakar da ta gabata.

Dan wasan PSG, Dembele.
Hoton Dembele lokacin da PSG ta dauki kofin Zakarun nahiyar Turai Hoto: Ousmane Dembele
Source: Facebook

Takaitaccen jawabin da Dembele ya yi

Dembele, wanda ke jinyar rauni a halin yanzu, ya halarci bikin bayar da kyautar a birnin Paris, sai dai hawaye ya zuba daga idanunsa yayin da ya daga kyautar tasa ta tarihi, in ji rahoton Sky Sport.

“Mahaifiyata, ina so na gode miki, kin kasance tare da ni koyaushe, mama, ki na gefe na a kowane lokaci.”
“Ga iyalina, mun fuskanci abubuwa da dama tare. Mun sha wuya tare, mun yi farin ciki tare. Za mu kasance tare koyaushe.”

- In ji Dembele bayan ya jarbi kambun.

Malami ya yi hasashen nasarar Arsenal

A wani labarin, kun ji cewa Malamin coci, Joel Atuma ya yi hasashen cewa kungiyar kwallon kafa ta Arsenal za ta kai wasan karshe a Champion na bana.

Kara karanta wannan

Abin fashewa ya tarwatse a masana'antar sojojin Najeriya, an rasa rayuka

Malamin ya ce Arsenal za ta doke PSG a wasan kusa da karshe sannan ta fafata da Barcelona a wasan karshe na gasar cin kofin zakarun nahiyar turai.

Ya kuma kara da cewa a iya abin da ya hango, Arsenal za ta doka Barcelona ta daukin kofin a wannan kakar wasa da ake ciki.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262