'Dan Sandan Najeriya Ya Rasu a Gidan Kallon Kwallo ana Wasan Arsenal da Real Madrid

'Dan Sandan Najeriya Ya Rasu a Gidan Kallon Kwallo ana Wasan Arsenal da Real Madrid

  • Wani sufeto na ƴan sanda ya faɗi matacce ana tsaka da wasan Arsenal da Real Madrid a Kalaba, babban birnin jihar Kuros Riba
  • Abokinsa da ya nemi a sakaya sunansa ya ce tare suke kallo kwallon kuma ɗan sanda ya yi murnar kowace kwallo da Arsenal ta jefa a ragar Madrid
  • Ya ce sai da aka tashi wasan sannan suka fahimci ba ya motsi a kujerar da yake zaune, suka garzaya da shi asibiti amma aka tabbatar da ya mutu

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Calabar, Cross River - Wani Sufetan 'Yan Sanda mai suna Stephen Enang ya fadi ya mutu a gidan kallon wasan da Arsenal ta doke Real Madrid da ci 3-0 a daren ranar Talata.

Jami'in ɗan sandan wanda ya kai matsayin sufeta ya rasa ransa ne bayan kammala kallon wasan Arsenal da Real Madrid a Kalaba, babban birnin jihar Kuros Riba.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai hari kan daliban jami'a a Kebbi cikin dare

Yan sanda.
'Dan Sanda ya mutu a gidan kallon wasan Arsenal da Real Madrid Hoto: @PoliceNG
Asali: Twitter

Jaridar The Natiton ta tattaro cewa marigayi Enang, dan asalin garin Ekori ne da ke karamar hukumar Yakurr a Jihar Kuros Riba a Kudancin Najeriya.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Bayanai sun nuna cewa yana aiki ne a ofishin 'yan sanda na Akim da ke kan titin IBB a birnin Kalaba.

Mutanen da suka san ɗan sandan sun bayyana shi a matsayin mutum mai nutsuwa kuma ɗan a mutun masoyin kungiyar ƙwallon ƙafa ta Arsenal da ke ƙasar Ingila.

Ta ya ɗan sanda ya mutu a gidan kallo?

Wani abokin ɗan sandan, wanda ya nemi a boye sunansa, ya bayyana cewa Enang yana cikin farin ciki a lokacin kallon wasan a wani gidan kallo da ke titin Abang-Asang.

“Yana cikin walwala sosai kuma lafiyarsa ƙalau, ya yi murna da shewa ta ƴan kallo a kowanne kwallo da Arsenal zura a ragar Madrid."
“Amma bayan tashi daga wasan, lokacin da kowa ke tafiya, muka lura cewa Stephen bai tashi daga kujerarsa ba kamar yadda sauran suka yi. A nan ne muka gane akwai matsala.”

Kara karanta wannan

Bayan kashe mutane sama da 50, gwamna ya gano waɗanda ke ɗaukar nauyin ta'adi

Declan Rice/Arsenal
'Dan sandan ya yi murna nasarar Arsenal kafin ya mutu Hoto: Arsenal
Asali: Getty Images

Yadda aka yi kokarin ceto ɗan sandan

Mutumin ya bayyana cewa an yi ƙoƙarin kai shi asibiti domin ceto rayuwarsa amma rai ya yi halinsa, kamar yadda PM News ta kawom

"A kujerar ya faɗi, muna ta magana amma ba ya ko motsi balle ya amsa, nan dai aka garzaya da shi zuwa Asibitin 'Yan Sanda da ke Akim.
"Duk kokarin da aka yi domin ceto rayuwarsa ya ci tura, daga baya aka tabbatar da cewa ya mutu.
“Shi mutum ne mai halin kirki, mai son kwallon kafa, kuma masoyin Arsenal ne na gaske. Wannan labari ya girgiza mu matuka,” in ji abokinsa.

Duk kokarin da aka yi na tuntubar Jami’ar Hulda da Jama’a na Rundunar 'Yan Sanda ta Jihar Kuros Riba, SP Irene Ugbo, bai yi nasara ba, domin ba ta amsa kiran waya ko sakonnin da aka aika mata ba.

An kashe mai goyon bayan Manchester United

Kara karanta wannan

Yadda Dutsen Tanshi ya dawo Najeriya daga Indiya duk da tsananin rashin lafiya

A wani labarin, kun ji cewa wani matashi ya kashe abokinsa kan wasan kwallon da aka fafata tsakanin Liverpool da Manchester United.

An tattaro cewa matashin wanda ke son Arsenal ya hallaka ɗan Manchester United saboda ya yi murnar kwallom da Mohammed Salah ya jefa a raga.

Wannan lamarin ya faru ne Kyobugombe da ke Yammacin ƙasar Uganda bayan wata zazzafar muhawara da ta haɗa su.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262