Albashin ma'aikata
ASUU ta fara janye ayyuka a jami'o'in Najeriya saboda jinkirin albashin watan Yuni, 2025, ta ce za ta aiwatar da tsarin "ba albashi, babu aiki" har sai an biya su.
A labarin nan, za a ji cewa ƙungiyar ƙwadago ta ƙasa ta shirya tsaf domin rufe Dukkanin wasu sassan aiki a babban birnin Abuja kan watsi da lamarin ma'aikata.
Gwamnatin jihar Jigawa ta rike albashin malamai 239 da suka yi watsi da aikinsu. An umurci wani mai gari da ya mayar da albashin shekara 3 da bai yi aikin ba.
Malaman jami'a sun koka kan rashin samun albashin watan Mayu bayan kusan mako daya da karewar wata. Abdelghaffar Amoka ya ce sun shiga sallah ba albashi.
Gwamnatin jihar Jigawa ta samu nasarar tsaftace bangaren ma'aikatanta. Gwamnatin ta gudanar da bincike inda ta gano dubunnan ma'aikata na bogi da ke karbar albashi.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince a biya ma'aikata da 'yan fansho kudade don su gudanar da bukukuwan babbar Sallah a cikin walwala da jindadi.
Gwamna Fintiri ya fara biyan sabon mafi karancin albashi na N70,000 ga ma'aikatan kananan hukumomin Adamawa. Ya ware ₦5bn don biyan hakkokin masu ritaya.
Ma’aikatan shari'a karkashin JUSUN sun rufe kotuna a Ibadan, a wani mataki na yajin aiki. Sun bukaci gwamnati ta kara masu albashi da alawus da 25% da 35%.
Gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya shirya gwangwaje ma'aikata don bukukuwan babbar Sallah. Gwamnan ya umarci a biya su albashin watan Yunin 2025.
Albashin ma'aikata
Samu kari