Jami'o'in Najeriya
Sakamakon kura-kuran fasahar na'ura da aka samu, sama da dalibai miliyan ɗaya da rabi suka kasa samun sama da maki 200 a UTME 2025. JAMB ta dauki mataki.
Za ku ji cewa jami’ar Maryam Abacha ta rufe dakunan kwanan dalibai mata biyu a Kano bisa zargin lalata da kin bin doka, tare da gargadi ga dalibai da iyayensu.
Rikici ya barke a jami'ar Katsina kan zaɓen VC. 'Yan takara sun soki zaɓen, sun zargi shugaba mai barin gado da nuna son zuciya domin wanda yake so ya samu nasara.
Gwamnan Bauchi na shan suka kan cewa karatun Boko shirme ne a wani bidiyo. Dr Kabiru Danladi Lawanti ya soki gwamna Bala Mohammed kan maganar da ya yi.
JAMB ta saki sakamakon UTME 2025. Fiye da dalibai miliyan 1.5 sun samu kasa da 200, 420,415 sun samu sama da 200. Ana iya duba sakamako ta yanar gizo ko SMS.
JAMB ta fitar da sakamakon UTME 2025, ta riƙe na dalibai 39,834 saboda kura-kurai. Ana binciken dalibai 80 bisa maguɗi, inda Anambra na kan gaba a wadanda ake zargi.
'Yan sanda sun cafke wata dalibar jami'ar Ekiti bisa zargin yin garkuwa da kanta domin ta sha soyayya da saurayinta. Kwamishinan 'yan sanda ya ce za a kai ta kotu.
ICPC na binciken batan biliyan 71 daga shirin ba da rancen karatu ga daliban manyan makarantu na asusun NELFUND, inda hukumar ta gayyaci jami'an gwamnati da na CBN.
Shugabannin kungiyar daliban Arewacin Najeriya a jihohi 19 sun ziyarci Atiku Abubakar a gidansa da ke Abuja. Atiku ya ce zai yi aiki tare da matasa wajen gina kasa.
Jami'o'in Najeriya
Samu kari