Masu Garkuwa Da Mutane
Yan bindiga sun shiga kauyen Dawaki a kusa da Bwari a Abuja, sun ɗauki mutane da dama amma ƴan sanda sun kai ɗauki kuma ana tsammanin sun ceto mutanen.
Yan bindiga sun kai hari anguwar Shagari da ke Dei- Dei a birnin tarayya Abuja tare da yin garkuwa da jami'in kwastam da matarsa da 'ya'yansa guda uku.
Rundunar 'yan sanda a jihar Akwa Ibom ta tabbatar da sace basarake, Ogwong A Abang a jihar a daren jiya Asabar 18 ga watan Mayu bayan sun kutsa kai cikin fadarsa.
Wata kungiya a jihar Neja ta bayyana halin da matan da yan bindiga suka kashe mazajensu suka shiga a kauyuka sama da 80 a karamar hukumar Mariga ta jihar Neja.
Yan sandar Najeriya sun kama gungun masu garkuwa da mutane a jihar Delta. Cikin mutane ukun da aka kama daya ya ce ya zo Najeriya ne daga kasar waje.
Rundunar ‘yan sanda a jihar Anambra ta ce ta kaddamar da farautar wadanda suka yi garkuwa da Basil Chukwuemeka, wani babban limamin cocin Katolika a jihar.
A yayin da matsalar tsaro ke kara ci wa gwamnati tuwo a kwarya, Ministan tsaro, Mohammed Badaru ya yi kira ga kungiyar tarayyar Turai da ta tallafawa Nigeria.
Tsagerun ƴan bindiga sake kai hari kauyen Yar Malamai jim kaɗan bayan jami'an tsaro sun tashi, sun sace mutane da yawa tare da tafka ɓarna ranar Litinin.
Rundunar haɗin guiwa da ta kunshi sojoji, ƴan snada, dakarun ƴan sa'kai na Radda da mafarauta sun yi nasarar ceto fasinjoji 17 daga ƴan bindiga a jihar Katsina.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari