Zaben jihohi
Hukumar INEC ta sanar da cewa za a yi zaben gwamnoni a jihohin Ekiti da Osun a Yuli da Agusta a 2026. Shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu ne ya sanar da haka.
Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya bayyana cewa shi da takwarorinsa ba za su yarda a rusa hukumomin zaɓen jihohi ba, ya ce INEC kanta tana fuskantar matsala.
Gwamna Abdullahi Sule zai nemi kujerar Sanatan Nasarawa ta Arewa a 2027. An bayyana cewa gwamnan tuni ya kafa kwamitin da zai shirya neman takararsa.
Wasu yan APC a Kaduna sun nemi Shugaba Tinubu da Gwamna Uba Sani da su fara shirin tsayawa takara a 2027, domin za su samu goyon bayansu a rumfunan zabe.
Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa ya bayyana cewa ba shi da niyyar tsayawa takarar gwamnan Kano ko Sanata a 2027, yana mai cewa ya fi karkata ga hidimar jama'a.
A wannan labarin, KNIYA ta bukaci Sanata Barau Jibrin ya tsaya takarar gwamna a 2027, tana mai cewa yana da nagarta da hangen nesa don dawo da martabar Kano.
Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tanadi hukunci kan shari'o'in da ke neman tsige gwamnan Edo. PDP na kalubalantar nasarar APC, inda ta ce akwai kuskure a zaben.
An shiga jimami bayan Alhaji Abdulkadir Yusuf Guɗe, tsohon ɗan takarar gwamnan Kano kuma jigo a PDP da NRO, ya rasu da safiyar Juma’a yana da shekaru 63.
Sanata Buhari ya ce zai tsaya takarar gwamnan Oyo a 2027. Ya gaji da majalisa, ya ce ko an kawo tikitin sanata ba zai tsaya ba domin mutan ke son ya yi gwamna.
Zaben jihohi
Samu kari