Yan bindiga
'Yan bindiga sun hallaka mataimakin magatakardar Kwalejin Gwamnatin Tarayya da ke jihar Ebonyi, an kashe Innocent Obi ne a gidansa da ke jihar Imo.
Miyagun ƴan bindiga sun yi kwanton ɓauna kan tawagar ƴan sakai a jihar Bauchi. Ƴam bondigan sun halaka ƴan sakai mutum tara tare da raunata wasu daban.
Wani mai garkuwa da mutane, Gaiya Usman da jami'an 'yan sanda su ka kama ya bayyana cewa duka kudin fansa Naira dubu 470 kayan sakawa ya siya da su.
Miyagun ƴan bindiga sun halaka mutum uku a wani sabon hari da suka kai a ƙaramar hukumar Logo ta jihar Benue. Al'ummar yankin sun buƙaci gwamnati ta kai musu ɗauki.
Dakarun sojojin Najeriya na Operation Hadarin Daji sun samu nasarar ceto ɗaliban jami'ar gwamnatin tarayya Gusau (FUGUS) da ke jihar Zamfara da aka sace.
Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya bayyana kuɗin fansan da ƴan bindiga suka ƙarba kafin su sako ɗaliban jami'ar jihar da suka yi awon gaba da su.
Ƴan bindiga sun sake kai farmaki cikin tsakar dare a jami'ar gwamnatin tarayya ta Gusau (FUGUS) da ke jihar Zamfara. Ƴan bindigan sun sace ɗalibai guda biyu.
Wasu 'yan bindiga sun kai farmaki kan wata motar bas ta fasinja a jihar Benue inda su ka yi ajalin mutum daya tare da raunata wasu mutane guda biyu a wani sabon hari
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar halaka wani ɗan bindiga har lahira tare da ceto wasu mutum shida da aka yi garkuwa da su a jihar Kaduna.
Yan bindiga
Samu kari