Aikin Hajji
Hukumar kula da alhazai ta jihar Kwara ta ce ranar ƙarshe ta biyan kuɗin Hajjin 2025 ita ce Janairu 31, 2025. An nemi alhazai su gabatar da fasfo kafin Fabrairu 25.
Hukumar NAHCON ta ce maniyyata aikin hajjin 2025 za su samu tallafin $500. Shugaban hukumar, Farfesa Abdullahi ya fadi matsalolin da aka samu a shekarar 2024.
Hukumar jin dadin Alhazai ta kasa (NAHCON), ta sanya lokacin da maniyyata za su kammala biyan kudaden Hajji na shekarar 2025. NAHCON ta ce ba za ta yi kari ba.
NAHCON ta amince da Naira miliyan 8.7 a matsayin kudin aikin Hajjin 2025 ga maniyyatan Kudu, sai Naira miliyan 8.3 ga 'yan Arewa maso Gabas. Ta yi karin bayani.
NAHCON ta sanar da cewa gwamnati ta zabi jirage 4 don jigilar alhazai a aikin Hajjin 2025. Haka zalika, hukumar ta cimma yarjejeniya da kasar Saudiyya.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya roki alfarma wajen shugaba Bola Ahmed Tinubu domin rage kudin aikin hajjin 2025 saboda matsin tattalin arziki da ake fuskanta
Babban Limamin Cocin RCCG, Pastor Enoch Adeboye, ya musanta hoton da ake yaɗawa na fasahar AI da ya nuna shi a matsayin Alhaji inda ya ce ba gaskiya ba ne.
Hukumar Kula da Alhazan Kaduna ta fara biyan N61,080 ga Alhazai 6,239 da suka yi aikin Hajj a 2023, bayan matsalar wutar lantarki da ta faru a Muna.
Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) ta shirya daina amfani da Dala wajen biyan kudaden abubuwan da suka shafi aikin Hajji. Ta ce hakan zai rage tsadar aikin Hajji.
Aikin Hajji
Samu kari