An Zabi Sabon Shugaban ADC a Kano bayan Shigar Kwankwaso, Mutane 27 Sun Samu Mukami

An Zabi Sabon Shugaban ADC a Kano bayan Shigar Kwankwaso, Mutane 27 Sun Samu Mukami

  • Jam'iyyar ADC ta zabi sababbin shugabanni a matakin jihar Kano yayin da take shirye-shiryen tunkarar babban zaben 2027 mai zuwa
  • Abdullahi Maikano Tarauni, wanda ake ganin yana da kusanci da Rabiu Kwankwaso a siyasa, ya zama sabon shugaban ADC na Kano
  • An kuma zabi sauran mambobin kwamitin gudanarwa na ADC (NWC) reshen jihar a taron da ya gudana ranar Lahadi da ta gabata

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jihar Kano - Jam’iyyar ADC ta zabi Abdullahi Maikano Tarauni, wanda ake ganin na kusa da Rabiu Musa Kwankwaso ne, a matsayin sabon shugaban jam’iyyar a jihar Kano.

Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan tsohon dan takarar shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso ya sauya sheka daga NNPP zuwa jam'iyyar ADC.

Jam'iyyar ADC.
Tambarin jam'iyyar da yan adawar Najeriya suka yi hadaka a ciki, ADC Hoto: ADC Party
Source: Twitter

Jaridar Leadership ta tattaro cewa an gudanar da zaben ne a taron jam’iyyar na jiha da aka yi ranar Lahadi, inda aka kuma fitar da sababbin shugabannin jam’iyyar a matakin jiha.

Kara karanta wannan

Tsohon ɗan takarar gwamna ya ragewa NNPP ƙarfi a Katsina gabanin 2027

Jerin sabqbbin shugabannin ADC a Kano

Haka zalika an zabi Hon. Ali Datti Yako daga Kiru a matsayin mataimakin shugaban jam'iyya na jihar Kano. Sauran wadanda suka shiga kwamitin gudanarwa na ADC jihar sun hada da:

1. Hon. Ali Shettima (Nassarawa) – mataimaki na farko

2. Hon. Bashir Kofa (Bebeji) – mataimaki na biyu

3. Hon. Bello Yandadi (Ghari) – mataimaki na uku

4. Dr. Bala Muhammad Inuwa (Takai) – sakataren ADC

5. Dr. Haruna Rogo (Rogo) – mataimakin sakatare

6. Hon. Abba Muktar (Danbatta) – ma’aji

7. Hon. Balarabe Sarki (Bichi) – mataimakin ma’aji

8. Farfesa Salis Muhammad – sakataren kudi

9. Hon. Nura Makoda – mataimakin sakataren kudi

10. Hon. Shehu Kabo – sakataren yada labarai

11. Hon. Magaji Ya’u Indabawa (Kano Municipal) – mataimakin sakataren kudi

12. Barista Muhammad Yahaya (Kura) – mai ba da shawara kan shari’a

13. Barista Tahir Ibrahim Yakasai – mataimakin mai ba da shawara kan shari'a

Kara karanta wannan

APC na tsakiyar zawarcin Shekarau, Tinubu zai narka kusan Naira biliyan 4 a Kano

14. Hon. Yusuf Bature (Nassarawa) – sakataren walwala

15. Hon. Kabiru Garba Abba (Sumaila) – mataimakin sakataren walwala

16. Hon. Sunusi Surajo (Madobi) – sakataren tsare-tsare

17. Hon. Alu Karaye (Karaye) – mataimakin sakataren tsare-tsare

18. Hon. Sa’adu Zangon Mata (Dawakin Tofa) – Audita Janar

19. Dr. Shehu Ibrahim Bawa (Tarauni) – mataimakin Audita Janar

20. Hon. Ahmad Maikoriya (Dawakin Kudu) – shugaban masu bukata ta musamman

21. Hon. Farida Kamba (Ungoggo) – shugabar mata

22. Hon. Hauwa Awaisu (Shanono) – mataimakiyar shugabar mata

23. Hon. Sunusi Oscar (Fagge) – shugaban matasa

24. Hon. Abba Abdulhamid (Kumbotso) – mataimakin shugaban matasa

25. Hon. Mustapha Bala Getso (Gwarzo) – mai tsawatarwa

26. Hon. Bashir Tijjani Maisango (Nassarawa) – mataimakin mai tsawatarwa.

Nasir Gawuna.
Nasiru Yusuf Gawuna, Kwamared AminuAbdussalam Gwarzo da tsohon dan takarar shugaban kasa, Rabiu Kwankwaso a taron ADC na Kano Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso
Source: Facebook

ADC na shirye-shiryen zaben 2027

Kwankwaso ya tabbatar da hakan a wani sako da ya wallafa a shafin Facebook, inda aka gan shi ya halarci taron zaben shugabannin ADC.

Zaben wadannan sababbin shugabanni na ADC na zuwa ne a daidai lokacin da siyasar Kano ke kara zafi, musamman yayin da ake shirin tunkarar zaben 2027.

Kara karanta wannan

Siyasar 2027: Atiku da Kwankwaso na cikin matsala, ADC ta sake darewa gida 2

Sabon bangare ya bulla a jam'iyyar ADC

A wani rahoton, kun ji cewa rikicin jam'iyyar ADC mai adawa a Najeriya ya kara tsananta bayan bullowar sabon bangare ana shirin zaben 2027.

Sabon tsagin ya bayyana cewa ba ya goyon bayan bangaren David Mark ko na Nafiu Bala, yana mai cewa yana wakiltar sahihan shugabannin jam’iyyar ADC.

Jagoran sabon bangaren, Don Norman Obinna, ya yi ikirarin cewa su ne halastattun mambobin kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da aka zaba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262