APC da ADC Sun Kece Raini yayin da 'Yan Majalisar Tarayya 27 Suka Sauya Sheka

APC da ADC Sun Kece Raini yayin da 'Yan Majalisar Tarayya 27 Suka Sauya Sheka

  • Majalisar wakilai ta shaida sauya shekar 'yan majalisu 27 zuwa jam'iyyun APC, ADC sakamakon rikicin cikin gida a tsofaffin jam'iyyunsu
  • Jam'iyyar APC ta samu karin mambobi 14, ciki har da 'yan majalisu 10 daga jam'iyyar NNPP, wadanda dukka suka fito daga jihar Kano
  • Legit Hausa ta tattaro sunayen 'yan majalisun 27 da jam'iyyun da suka koma, yayin da ake tunkarar kakar zabe ta shekarar 2027

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja - A wani gagarumin sauyi na siyasa gabanin babban zaɓen 2027, an samu sauya sheƙar ɗumbin ƴan majalisar wakilan Najeriya zuwa jam'iyyun ADC, APC, da sauran su.

Shugaban majalisar, Tajudeen Abbas, ne ya karanta wasiƙun sauya sheƙar ƴan majalisu 27 yayin zaman majalisar, matakin da ake ganin zai sauya taswirar siyasar ƙasar nan.

'Yan majalisa 27 sun sauya sheka zuwa jam'iyyu daban daban
Zauren majalisar wakilan Najeriya da ke Abuja. Hoto: @HouseNGR
Source: Facebook

'Yan majalisa 27 sun sauya sheka

Kara karanta wannan

Kwankwaso, Atiku, Obi sun hade kai, sun shirya kayar da Tinubu a zaben 2027

Mafi yawan waɗanda suka sauya sheƙar sun bayyana cewa rikicin cikin gida da rarrabuwar kai a tsofaffin jam'iyyunsu ne ya tilasta musu neman mafita, in ji rahoton Channels TV.

Babban abin lura a wannan sauya sheƙar shi ne yadda APC ta samu gagarumar nasara a Kano, inda ƴan majalisu 10 daga jam'iyyar NNPP suka koma cikinta.

Daga cikin waɗanda suka koma APC har da mataimakin shugaban marasa rinjaye na majalisar, Aliyu Madaki (Dala) da kuma Tijjani Abdulkadir Jobe (Tofa/Dawakin-Tofa).

Karuwar tagomashi ga jam'iyyar ADC

Jam'iyyar hadakar 'yan adawa ta ADC ta fito a matsayin gidan adawa mai ƙarfi, inda ta karɓi ƴan majalisu takwas daga jam'iyyun PDP da LP.

Daga cikin waɗanda suka shiga ADC har da George Ozodinobi (Anambra) da Abdussamad Dasuki (Sokoto), matakin da ke nuna cewa jam'iyyar tana ƙara samun karɓuwa.

Wannan yana zuwa ne kwanaki kaɗan bayan da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso da Peter Obi suka fara nuna alamun haɗa kai a ƙarƙashin inuwar jam'iyyar ta ADC domin fuskantar zaɓen 2027.

Sabon tsarin siyasa a sauran jihohi

Kara karanta wannan

A ƙarshe, Kwankwaso ya yanki katin zama ɗan jam'iyyar ADC, ya haɗe da su Atiku

Baya ga manyan jam'iyyun biyu, jam'iyyar Accord ta samu ƴan majalisu biyu daga jihar Osun, yayin da sabuwar jam'iyyar APP ta samu ƴan majalisu biyu daga jihohin Imo.

Wani abin mamaki shi ne sauya sheƙar Philip Agbese daga jam'iyyar APC mai mulki zuwa jam'iyyar LP, matakin da ya sa aka rinka tattaunawa a harabar majalisar, in ji rahoton Punch.

Jam'iyyun ADC da APC sun samu karuwa a sauya shekar 'yan majalisar wakilai 27
Rt. Hon. Tajudeen Abbas ya na jagorantar zaman majalisar wakilan Najeriya. Hoto: @HouseNGR
Source: Twitter

Jerin 'yan majalisun da suka sauya sheka

Sunayen 'yan majalisa

Tsohuwar jam'iyya

Sabuwar jam'iyya

Mazaba/Jiha

1

Aliu Madaki

NNPP

APC

Dala (Kano)

2

George Ozodinobi

LP

ADC

Njikoka/Anaocha/Dunukofia (Anambra)

3

Philip Agbese

APC

LP

Ado/Okpokwu/Ogbadibo (Benue)

4

Ugochinyere Michael Ikeagwuonu

PDP

APP

Ideato (Imo)

5

Abdussamad Dasuki

PDP

ADC

Kebbe/Tambuwal (Sokoto)

6

Tijjani Abdulkadir Jobe

NNPP

APC

Tofa/Dawakin-Tofa/Rimingado (Kano)

7

Seyi Sowunmi

LP

ADC

Ojo (Lagos)

8

Mohammed Bassi

PDP

APC

Mayo Belwa/Ganye/Jada/Toungo (Adamawa)

9

Ghali Tijjani Mustapha

NNPP

APC

Ajingi/Albasu/Gaya (Kano)

10

Shehu Bello

NNPP

APC

Fagge (Kano)

11

Dankawu Idris

NNPP

APC

Kumbotso (Kano)

12

Hussain Hassan Shehu

NNPP

APC

Nassarawa (Kano)

13

Rabiu Yusuf

NNPP

APC

Sumaila/Takai (Kano)

14

Garba Mohammed Chiroma

NNPP

APC

Gezawa/Gabasawa (Kano)

15

Ibrahim Mohammed (Kano)

NNPP

APC

Gwale (Kano)

16

Jaafaru Yakubu

PDP

APC

Bali/Gassol (Taraba)

17

Sadiq Abbas Tafida

PDP

APC

Jalingo/Yorro/Zing (Taraba)

18

Ibrahim Mohammed (Kebbi)

PDP

APC

Birnin-Kebbi/Kalgo/Bunza (Kebbi)

19

Bello Shinkafi

PDP

APC

Shinkafi/Zurmi (Zamfara)

20

Harris Okonkwo

LP

ADC

Idemili ta Arewa/Kudu (Anambra)

21

Yaya Bauchi Tongo

PDP

ADC

Gombe/Kwami/Funakaye (Gombe)

22

Mustapha Abdullahi

APC

ADC

Ikara/Kubau (Kaduna)

23

Mani Maishinko Katami

PDP

ADC

Binji/Silame (Sokoto)

24

Umar Yusuf Yabo

PDP

ADC

Yabo/Shagari (Sokoto)

25

Nwogu Mathew

LP

APP

Aboh Mbaise/Ngor Okpala (Imo)

26

Akanni Clement Ademola

PDP

Accord

Boluwaduro/Ifedayo/Ila (Osun)

27

Oladebo Lanre Olomololaye

PDP

Accord

Ayedaade/Irewole/Isokan (Osun)

Kara karanta wannan

Jerin manyan Najeriya da suka halarci jana'izar mamar El Rufa'i

'Yan majalisar Kano sun yi taron sirri

A wani labari, mun ruwaito cewa, ‘yan majalisar wakilai daga yankin Kano ta Kudu sun gudanar da abin da suka kira muhimmin taro a ranar Litinin, 30 ga watan Maris, 2026.

Sun zauna ne domin tattauna makomar siyasarsu, yayin da suke bayyana rashin jin dadinsu game da jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Wasu daga cikin wadanda suka halarci taron sun haɗa da manyan ‘yan majalisar wakilai kamar Alhassan Doguwa, Kabiru Rurum, Abdulmumin Jibrin da Abdullahi Rogo.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com