Magana Ta Kare, Gwamna Dauda Lawal Ya Bi Sahun Abba Gida Gida, Ya Sauya Sheka zuwa APC

Magana Ta Kare, Gwamna Dauda Lawal Ya Bi Sahun Abba Gida Gida, Ya Sauya Sheka zuwa APC

  • Mataimakin gwamnan Zamfara, Mani Malam Mummuni ya kawo karshen jita-jitar da ake yadawa kan shirin Gwamna Dauda Lawal na komawa APC
  • Rahotanni sun nuna cewa Mani ya sanar da ficewar Gwamna Dauda Lawal tare da mukarrabansa, daga PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya
  • Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya raba gari da jam'iyyar NNPP, tare da komawa APC gabanin zaben 2027

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zamfara, Nigeria - Rahotanni daga jihar Zamfara na nuna cewa Gwamna Dauda Lawal ya fice daga jam'iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya.

Mataimakin gwamnan Zamfara, Mani Malam Mummuni ne ya sanar da hakan a madadin Gwamna Dauda Lawal yau Litinin, 9 ga watan Maris, 2026.

Gwamna Dauda Lawal.
Gwamna Dauda Lawal na jagorantar zama da kwamishinoni a fadar gwamnatin Zamfara Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Wani mai amfani da kafar sadarwa ta Facebook, Imran Muhammad ne ya wallafa bidiyon da aka ji mataimakin gwamnan Zamfara na sanar da komawarsu APC.

Kara karanta wannan

Bayan Dauda Lawal, an gano gwamnoni 2 da ake hasashen za su bar PDP

A sakon da ya walllafa tare da wani gajeren faifan bidiyo, Imran Muhammad ya ce:

"Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Mani Malam Mummuni, a madadin Gwamna Dauda Lawal, ya sanar da sauya shekarsu daga PDP zuwa jam'iyyar APC.

A faifan bidiyon, wanda bai wuce dakika 36 ba, an ji Mani Malam Mummuni na mabtar APC a wurin wani taro a fadar gwamnatin Zamfara da ke birnin Gusau.

Haka zalika, mataimakin gwamnan ya umarci duka mahalarta taron da du mike tsaye, domin nuna goyon bayansu ga wannan sauya sheka zuwa APC.

Har kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani daga gwamnatin Zamfara kan wannan ci gaban, amma dai wasu majiyoyi da dama suk jima suka ikirarin sauya shekar Gwamna Lawal.

Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sauya sheka daga jam'iyyar NNPP zuwa APC mai mulki.

Karin bayani na nan tafe...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262