Magana Ta Kare, Gwamna Dauda Lawal Ya Bi Sahun Abba Gida Gida, Ya Sauya Sheka zuwa APC
- Mataimakin gwamnan Zamfara, Mani Malam Mummuni ya kawo karshen jita-jitar da ake yadawa kan shirin Gwamna Dauda Lawal na komawa APC
- Rahotanni sun nuna cewa Mani ya sanar da ficewar Gwamna Dauda Lawal tare da mukarrabansa, daga PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya
- Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya raba gari da jam'iyyar NNPP, tare da komawa APC gabanin zaben 2027
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Zamfara, Nigeria - Rahotanni daga jihar Zamfara na nuna cewa Gwamna Dauda Lawal ya fice daga jam'iyyar adawa ta PDP zuwa APC mai mulkin Najeriya.
Mataimakin gwamnan Zamfara, Mani Malam Mummuni ne ya sanar da hakan a madadin Gwamna Dauda Lawal yau Litinin, 9 ga watan Maris, 2026.

Source: Facebook
Wani mai amfani da kafar sadarwa ta Facebook, Imran Muhammad ne ya wallafa bidiyon da aka ji mataimakin gwamnan Zamfara na sanar da komawarsu APC.
A sakon da ya walllafa tare da wani gajeren faifan bidiyo, Imran Muhammad ya ce:
"Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Mani Malam Mummuni, a madadin Gwamna Dauda Lawal, ya sanar da sauya shekarsu daga PDP zuwa jam'iyyar APC.
A faifan bidiyon, wanda bai wuce dakika 36 ba, an ji Mani Malam Mummuni na mabtar APC a wurin wani taro a fadar gwamnatin Zamfara da ke birnin Gusau.
Haka zalika, mataimakin gwamnan ya umarci duka mahalarta taron da du mike tsaye, domin nuna goyon bayansu ga wannan sauya sheka zuwa APC.
Har kawo yanzu dai babu wani cikakken bayani daga gwamnatin Zamfara kan wannan ci gaban, amma dai wasu majiyoyi da dama suk jima suka ikirarin sauya shekar Gwamna Lawal.
Wannan na zuwa ne makonni kadan bayan gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sauya sheka daga jam'iyyar NNPP zuwa APC mai mulki.
Karin bayani na nan tafe...
Asali: Legit.ng
