Kwankwaso Ya Yi Magana bayan Ganawa da Gwamna PDP, Ya Tabo Abin da Suka Tattauna
- Jagoran NNPP na kasa, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya yi takaitacciyar magana bayan kammala tattaunawa da Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo
- Kwankwaso ya bayyana cewa yana da kyakkyawar alaka da Gwamna Makinde, wanda ke wa'adinsa na karshe a kan mulki
- Wannan na zuwa ne a lokacin da ake yada jita-jitar cewa akwai yiwuwar Gwamna Makinde da Kwankwaso su kulla kawance kafin zaben 2027
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Oyo, Nigeria - Da yammacin ranar Laraba, 25 ga watan Fabrairun 2026 aka samu labarin cewa tsohon dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya gana da Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde.
Rahotanni sun ce Kwankwaso da Makinde na PDP sun shiga wata tattaunawar sirri a ofishin gwamna da ke gidan gwamnatin Oyo a Ibadan.

Source: Facebook
Ganawar Kwankwaso da Makinde ta ja hankali
Jaridar Daily Trust ta ce wannan gannawar, wadda aka bayyana a hukumance a matsayin ziyarar ban girma, ta ja hankalin ‘yan siyasa sakamakon rade-raden da ake yi na yiwuwar kulla sabon kawance gabanin zaben 2027.
Kwankwaso ya samu rakiyar shugaban NNPP na kasa, Dr. Ajuji Ahmed; sakataren yada labarai na kasa, Ladipo Johnson; sakataren kwamitin amintattu, Buba Galadima; da sauran manyan jiga-jigai.
Abin da ya kai Kwankwaso jihar Oyo
Tawagar ta NNPP ta ziyarci jihar Oyo ne domin kaddamar da sabon ofishin jam’iyya na jiha da kuma tattauna batutuwan da suka shafi harkokin cikin gida ma jam’iyya.
Sai dai, ziyarar da ya kai wa Makinde, gwamna da ke wa’adi na biyu a karkashin inuwar jam’iyyar PDP, ta ja hankali sosai saboda bambancin jam’iyyun shugabannin biyu.
Tattaunawar sirrin ta dauki tsawon kusan sa’o’i biyu, kuma an yi ta ne ba tare da an bar yan jarida sun shiga don dauko rahoto ba.
Martanin Kwankwaso bayan ganawa da Makinde
Da yake magana da manema labarai bayan taron, Kwankwaso ya yi watsi da zargin cewa ziyarar tana da alaka da kulla kawance tsakanin jam’iyyun adawa.
A ruwayar Leadership, tsohon gwamnan ya ce:
“Wannan ziyarar ta fi mayar da hankali kan zumunci fiye da siyasar jam’iyya. Ni da Gwamna Makinde mun dade da sanin juna. Kafin mu wuce taron jam’iyyar mu a jihar, na ga ya dace na biyo na gaishe shi.”

Source: Facebook
Kwankwaso ya kuma waiwayi tarihin siyasarsa, inda ya bayyana cewa yana daya daga cikin wadanda suka kafa PDP a 1998, kuma an zabe shi a matsayin Gwamnan Jihar Kano a 1999 a karkashin jam’iyyar.
Ya tunatar da cewa ya taba yin Ministan Tsaro a gwamnatin PDP, sannan ya sake dawowa matsayin gwamna a 2011, kafin daga bisani ya ahiga APC, sannan kuma ya zama jagoran jam’iyyar NNPP na kasa.
Kwankwaso ya hadu da Gawuna a Kano
A wani rahoton, kun ji cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya hadu da tsohon dan takarar gwamnan Kano a jam'iyyar APC a zaben 2023, Nasiru Yusuf Gawuna.
Kwankwaso ya hadu da Dr Nasiru Yusuf Gawuna a filin jirgin saman kasa da kasa na Malam Aminu Kano da ke cikin birnin Kano.
Hakan na zuwa ne bayan madugun Kwankwasiyya ya kai ziyara gidan tsohon gwamna Malam Ibrahim Shekarau bisa rasuwar yayansa
Asali: Legit.ng


