"Bama Yi, Bama Yi," 'Dan Majalisar Tarayya Ya Sha da Kyar da Matasa Suka Yi Kansa a Kano

"Bama Yi, Bama Yi," 'Dan Majalisar Tarayya Ya Sha da Kyar da Matasa Suka Yi Kansa a Kano

  • Mutane sun fatattaki 'dan Majalisar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado, Hon. Tijjani Abdulkadir Jobe, daga wurin taron APC a mazabarsa
  • Bayanai sun nuna cewa tun da dan Majalisar ya ci zaben 2023, bai sake zuwa mahaifarsa Tofa ba sai a wannan karon
  • Fustattun matasa sun rika masa ihu a taron, lamarin da ya tilasta wa jami'an tsaro da magoya bayansa fitar da shi a mota

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Matasa sun yi wa dan majalisa wakilai mai wakiltar mazabar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado, Hon. Tijjani Abdulkadir Jobe, ihun bama yi tare da korarsa daga wurin taron APC.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a wurin taron mazaba na zaben shugabannin jam'iyyar APC a karamar hukumar Tofa da ke Jihar Kano.

Jobe.
Mamba mai wakiltar Dawakin Tofa/Tofa/Rimin Gado a Majalisar Wakilai, Hon. Tijjani Abdulkadir Jobe Hoto: Tijjani Abdulkadir Jobe
Source: Facebook

Yadda matasa suka fatattaki dan Majalisa

Kara karanta wannan

El Rufa'i ya shiga mugun hali hannun ICPC, jini ya rika zuba ta hancinsa ana azumi

Daily Trust ta tattaro cewa wasu bidiyoyi da ke yawo a kafafen sadarwa sun nuna gungun matasa suna fadin "bama yi, bama yi," tare da tunkarar wurin da 'dan Majalisar yake.

Lamarin ya faru ne yayin da Jobe yake jawabi a wurin taron wanda ya gudana garinsu na haihuwa, wato Tofa.

A daya daga cikin bidiyoyin, wanda Aminiya ta wallafa a Facebook, an ji muryar wani daga cikin taron yana cewa, "Wallahi akwai gyara. Mu maharba ba ka dube mu ba."

Sai dai lamarin ya rincabe ne yayin da wasu matasa suka ci gaba da ihu da fadin kalaman batanci.

Bidiyoyin sun nuna yadda hadimai, jami'an tsaro da magoya baya suka yi kokarin fitar da dan majalisar daga wurin taron a cikin mota.

A farkon wannan watan, Jobe ya nemi afuwar al'ummar mazabarsa kan duk wani kuskure da ya yi a lokacin taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar, taron da rahotanni suka ce ya kare cikin hargitsi.

An ruwaito cewa kujerar majalisar wakilai ta Dawakin Tofa/Rimin Gado/Tofa tana fuskantar zazzafar siyasa gabanin babban zabe mai zuwa, inda aka ce wasu fitattun jiga-jigan APC suna neman wannan kujera.

Kara karanta wannan

An fara fahimtar wadanda APC za ta zaba shugabannin jam'iyya na kasa a babban gangami

Jobe, wanda a halin yanzu yake wa’adi na biyar a Majalisar Wakilai, an ce yana da kusirin neman wa’adi na shida.

Komawarsa jam'iyyar APC kwanan nan ta ruruta jita-jitar cewa yana kokarin ganin ya samu tikitin takara kai tsaye a zabe mai zuwa.

An bayyana cewa taron na Tofa shi ne karon farko da dan majalisar ya bayyana a fili a garinsu tun bayan da ya lashe zaben wa'adi na biyar a shekarar 2023.

Wannan mazaba dai ta dade tana fitar da fitattun 'yan siyasa, wadanda suka hada da marigayi Danmasanin Kano, Dr. Yusuf Maitama Sule; da marigayi Dr. Maikano Rabiu.

Sauran sun hada da marigayi Mustapha Janguza; Engr. Hamisu Abubakar Lambu; da kuma Hon. Shehu Haruna Lambu.

NNPP ta yi zargin kama 'ya'yanta a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano ta yi Allah-wadai da kama daya daga cikin 'ya'yanta, Aiha K. Nass, da hukumomin tsaro suka yi a Kano.

Sakataren Yada Labarai na jam’iyyar NNPP a Kano, Injiniya Ibrahim Karaye, ya ce wannan abin takaici ne, kuma ya saba wa tsarin dimokuradiyya.

NNPP ta bukaci a saki Aiha K. Nass ba tare da ɓata lokaci ba saboda ‘yan kasa na da ‘yancin fadin albarkacin baki da kuma ‘yancin shiga kungiyoyi ko jam’iyyun siyasa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262