NNPP da Manyan Jam'iyyu 2 da ba a Ga Tambarinsu a Takardar Zaben Cike Gurbin Kano ba

NNPP da Manyan Jam'iyyu 2 da ba a Ga Tambarinsu a Takardar Zaben Cike Gurbin Kano ba

  • Hukumar zabe ta kasa (INEC) ba ta sanya jam'iyyun adawa uku, PDP, NNPP da ADC a zaben cike gurbin da ya gudana a jihar Kano ba
  • Rahotanni sun nuna cewa babu tambarin ko daya daga cikin wadannan jam'iyyu a takardar kada kuri'a da aka gani a zaben da ya gudana yau Asabar
  • Jam'iyyun sun zargi hukumar INEC da take hakkinsu na shiga zabe, suna mai cewa sun mika sunayen yan takararsu a hukumance

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Rahotanni daga jihar Kano sun nuna cewa babu tambarin manyan jam'iyyun adawa uku a takardun kada kuri'a na zaben cike gurbin yan Majalisu biyu a Kano.

A yau Asabar, 21 ga watan Fabrairu, 2026, Hukumar Zabe Ta Kasa, watau INEC ta gudanar da zabukan cike gurbi a karamar hukumar Ungogo da karamar hukumar Birni.

Kara karanta wannan

Ramadan: INEC ta hango abubuwa 2 da suka hana jama'a fitowa zaben cike gurbi a Kano

Amupitan.
Shugaban hukumar zabe ta kasa (INEC), Farfesa Joash Amipitan Hoto: INEC Nigeria
Source: Facebook

Jam'iyyun adawa 3 da babu a zaben Kano

Tashar Channels tv ta tattaro cewa manyan jam'iyyun adawa da ba a gani a takardar kada kuri'a ba sun hada da PDP, NNPP da kuma jam'iyyar hadaka watau ADC.

Legit Hausa ta fahimci cewa an shirya zaben ne domin cike kujeru biyu da suka zama babu kowa a Majalisar Dokokin Jihar Kano, sakamakon rasuwar ’yan majalisar da suka wakilci mazabun Kano Municipal da Ungogo a bara.

A wani taron manema labarai da aka gudanar kwanan nan, Kwamishinan Zaɓe na INEC a Kano, Abdul Zango, ya tabbatar da cewa duk jam’iyyu sun samu damar tsayar da ’yan takara, yana mai cewa hukumar ta shirya gudanar da zaɓe mai gaskiya da sahihanci.

Jam'iyyu 9 da suka fafata a zaben cike gurbi

Sai dai jerin sunayen ’yan takarar ƙarshe da INEC ta fitar ya nuna cewa jam’iyyu tara ne kawai aka tantance su, kuma babu PDP, NNPP da ADC a ciki.

Kara karanta wannan

Kano: Sauya shekar Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jawo tarnaki a jam'iyyar APC

Jam’iyyun da aka amince su shiga zaɓen sun haɗa da: Accord, ADP, APP, AAC, APC, APM, PRP, YPP, da jam'iyyar ZLP.

Duk da cewa INEC ba ta yi cikakken bayani kan dalilin cire manyan jam’iyyun ba,, jam’iyyun da abin ya shafa sun zargi hukumar da hana su amfani da haƙƙinsu na kundin tsarin mulki.

Zarge-zarge daga jam’iyyun da aka cire

A bangaren NNPP, wadda ke fama da rikice-rikicen cikin gida a Kano, an ruwaito cewa ɓangarori uku sun miƙa sunayen ’yan takara har guda shida a mazabun biyu, cewar Punch.

Sanata Mushud El-Jibril Doguwa, daga ɓangaren Boniface a NNPP, ya ce sun miƙa sunayen ’yan takararsu yadda ya kamata, amma INEC ta ƙi amincewa da jam’iyyar su ba tare da hujja ba.

NNPP.
Takardar kada kuri'a a zaben cike gurbin Kano da tambarin NNPP Hoto: Muhammad T. Umar, Saifullahi Hassan
Source: Facebook

A nasa ɓangaren, Shugaban PDP na Kano, Alhaji Yusuf Kibiya, ya zargi INEC da karya tanade-tanaden Dokar Zaɓe, yana mai cewa an ba su kwanaki huɗu kacal domin gudanar da zaɓen fidda gwani da miƙa sunayen ’yan takara.

Dalilin karancin masu kada kuri'a a Kano

A wani rahoton, kun ji cewa hukumar INEC ta danganta matsalar rashin fitowar jama'a a zaben Kano da lokacin azumin watan Ramadan da kumaNkarancin jam'iyyun da suka shiga takara.

Kara karanta wannan

Yadda zabe ke gudana a Kano da wasu sassan Najeriya a yau Asabar

Kwamishinan Zaɓe na Jiha (REC) na INEC a Jihar Kano, Abdu Zango, ne ya bayyana hakan yayin da hira da yan jarida lokacin da ya fita duba yadda zaben ke gudana.

A cewarsa, lokacin da aka gudanar da zaɓen na iya taka rawa wajen rage yawan masu kaɗa ƙuri’a, musamman ganin cewa ana cikin watan Ramadan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262