'Abin da Ya Sa Dole Arewa Ta Zabi Tinubu a 2027'; Shugaban APC
- Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya halarci wani gagarumin taron siyasa da aka shirya a jihar Nasarawa
- Farfesa Nentawe ya yi jawabi a wurin taron inda ya lissafo manyan ayyukan da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ke yi a Arewacin Najeriya
- Shugaban na APC ya kuma bayyana dalilin da ya sanya dole yankin Arewa ya goyawa shugaban kasar baya a zaben 2027
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Nasarawa - Shugaban jam’iyyar APC na kasa, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya kwararo yabo ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.
Farfesa Nentawe ya jinjina wa Shugaba Tinubu kan abin da ya kira ƙoƙarin kai Najeriya zuwa matsayi mai girma tun bayan karbar mulki a shekarar 2023.

Source: Facebook
Jaridar The Punch ta ce Farfesa Nentawe ya yi wannan bayani ne a Lafia, babban birnin jihar Nasarawa, ranar Alhamis, 12 ga watan Fabrairun 2026.

Kara karanta wannan
Bayan samun mukami, tsohon mai sukar Tinubu ya fadi abin da zai sa ya zarce a 2027
Ya yi bayanin ne yayin wani taron nuna goyon baya da aka shirya domin nuna godiya ga shugaban kasa da Gwamna Abdullahi Sule kan abin da masu shirya taron suka kira ayyukansu na gari.
Shugaban APC ya fadi ayyukan Tinubu a Arewa
Farfesa Nentawe ya kuma bayyana cewa gwamnatin Tinubu ta fi fifita yankin Arewa fiye da kowane yanki na kasar nan ta fuskar ayyukan ci gaba da ƙarfafa gwiwar al’umma.
Shugaban na APC ya buƙaci ’yan Arewa da su saka wa shugaban ta hanyar goyon bayan takararsa na sake tsayawa zaɓe a shekarar 2027.
"Shugaban kasa ya nuna cewa Najeriya za ta iya zama tsintsiya ɗaya madaurinta ɗaya. Ya nuna cewa gwamnati za ta iya zama mai haɗa kan kowa, kuma ya nuna cewa gwamnati za ta iya zama mai tsayin daka. Shi ya sa muke a wannan wajen."
“Muna da hanyar da ta tashi daga Sokoto zuwa Badagry, wadda za ta samar da madatsun ruwa sama da 60 don bar ruwa. Za ta samar da ci gaban noma, lantarki, da tsaftataccen ruwa. Wannan shi ne abin da shhugaban kasa yake samar mana a Arewa."
“Shugaban kasa yana samar da layukan dogo na jirgin kasa, wanda zai tashi daga Abuja zuwa Kano har zuwa Jamhuriyar Nijar."
"Ga dukkanmu a Arewa, hakan na nufin za mu zama masu shigo da kaya da fitar da su, domin daukacin yankin Arewacin Sudan, Burkina Faso, da Chadi za su dogara ne da mu wajen shigo da kayayyakinsu."
“Dukkan waɗannan ayyuka shugaban kasa ne yake yin su. Shi ya sa zai zama rashin adalci ga Arewa idan ba mu ba shi goyon baya ba, domin ba kowa ne zai iya samun ƙarfin gudanar da waɗannan ayyuka a gare mu ba kuma."
"Goyon bayan shugaban kasa ya zama dole ga Arewa saboda abubuwan da ya samar, abin da yake yi, da kuma abin da zai yi wa daukacin yankin.”
- Farfesa Nentawe Yilwatda

Source: Twitter
Nentawe ya jinjinawa gwamnan Nasarawa
Yayin da yake karbar dubun-dubatar mutanen da suka sauya sheka daga sauran jam’iyyun siyasa zuwa APC, shugaban ya kuma jinjina wa Gwamna Sule kan yadda yake samar da shugabanci na gari a jihar.
Ya nuna godiyarsa ga ayyukan samar da ababen more rayuwa a daukacin ƙananan hukumomin jihar guda 13, waɗanda suka haɗa da gadojin sama, hanyoyin cikin gari da na karkara, makarantu, asibitoci, da filin jirgin kasa da sauransu.

Kara karanta wannan
Abin da Shugaba Tinubu ya ce kan Shettima yayin da ake jita jitar sauya shi a 2027
Tinubu zai tarbi Gwamna Abba zuwa APC
A wani labarin kuma, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai tarbi Gwamna Abba Kabir Yusuf zuwa jam'iyyar APC.
Mai girma Bola Tinubu zai tarbi gwamnan ne a wani gagarumin biki da aka shirya gudanarwa a babban birnin jihar Kano.
Shugaban jam'iyyar APC na Kano ya bayyama cewa an kaddamar da kwamitocin da za su kula da shirin tarbar gwamnan.
Asali: Legit.ng
