Dan Majalisar PDP Ya Sauya Sheka zuwa Jam'iyyar APC, Ya Hadu da Gwamna Inuwa
- Jam'iyyar PDP mai adawa a jihar Gombe ta gamu da cikas bayan wani dan majalisar wakilai ya fice daga cikinta
- Dan majalisar wakilan ya sauya sheka zuwa jam'iyyar APC mai mulki tare da yin rajista don zama cikakken mamba
- Bayan shigarsa APC, dan majalisar wakilan ya gana da Gwamna Inuwa Yahaya wanda ya ba shi tabbacin cewa za a yi masa adalci a jam'iyyar
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Wani mamba a majalisar wakilan Najeriya, Hon. Abdullahi El-Rasheed (Bala Kelly), ya fice daga daga jam’iyyar PDP a jihar Gombe.
Dan majalisar ya sauya sheka zuwa jam’iyyar APC bayan ya fice daga PDP mai adawa a jihar Gombe.

Source: Facebook
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, Ismaila Uba Misilli ya fitar a ranar Alhamis, 12 ga watan Fabrairun 2026 a shafin Facebook.
Dan majalisa ya ziyarci Gwamna Inuwa
Dan majalisar, wanda ke wakiltar mazabar tarayya ta Dukku/Nafada, ya sanar da komawarsa APC ne yayin da ya ziyarci Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya a Abuja.
Ismaila Uba Misilli ya ce yayin ziyarar, Hon. El-Rasheed ya mika wa gwamnan katin zama dan jam’iyyar APC, wanda ya karba daga mazabarsa da ke karamar hukumar Dukku yayin aikin rijistar ’ya’yan jam’iyya ta yanar gizo da ake gudanarwa a yanzu.
Bala Kelly ya yabawa APC
Dan majalisar ya danganta matakinsa na shiga APC da salon jagoranci na gari na Gwamna Inuwa Yahaya, da manufofinsa masu alaka da jin dadin jama'a da kuma ayyukan ci gaba da ake gani a fadin jihar Gombe, da kuma shirin gyara na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Bala Kelly ya siffanta APC a matsayin wani dandali da ke da kyakkyawan matsayi na samar da ci gaba mai dorewa da shugabanci na gari, inda ya yi alkawarin cikakkiyar biyayya da kishin jam’iyyar da shugabancinta a karkashin Gwamna Inuwa Yahaya.
Me Gwamna Inuwa ya gaya masa?
A nasa martanin, Gwamna Inuwa Yahaya ya yi maraba da Hon. El-Rasheed zuwa cikin "masu ra'ayin ci gaba," inda ya yaba da jarumtarsa da kuma kwarin gwiwarsa.

Source: Facebook
Gwamnan ya tabbatar masa da cewa za a ba shi dukkan damammaki daidai da kowa, sannan ya bukace shi da ya yi aiki tare da sauran masu ruwa da tsaki na jam’iyyar domin ciyar da ajandar ci gaba ta APC, don amfanin mutanen mazabarsa, jihar Gombe, da ma Najeriya baki daya.
Sanatoci sun fice daga PDP zuwa APC
A wani labarin kuma, kun ji cewa wasu sanatoci na jam'iyyar PDP a jihar Taraba sun sauya sheka zuwa jam'iyyar APC.
Sanata Haruna Manu (Taraba ta Tsakiya) da Sanata Shuaibu Isa Lau (Taraba ta Arewa) bayyana cewa matsalolin cikin gida na PDP ya sanya suka fice daga jam'iyyar.
Sun jaddada cewa za su fi samun damar gudanar da ayyukan ci gaba ga al'ummarsa idan yana ƙarƙashin inuwar jam'iyya mai mulki ta APC.
Asali: Legit.ng

