Atiku ko Obi: El Rufai Ya Yi Maganar Wanda Zai Iya Samun Tikitin Takarar ADC a Zaben 2027
- Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma jigo a ADC, Nasir El-Rufai, ya ce jam'iyyar ba za ta yi amfani da tsarin karba-karba wajen tsaida dan takara ba
- Malam El-Rufai ya ce jam'iyyar ADC ta shirya tsaf a matakin farko kuma ta fara rijistar membobinta kafin gudanar babban taron jam'iyya na kasa
- Tsohon gwamnan ya ce jam'iyyar ADC ta shirya bayyana wani tsari na shugabanci kuma tana goyon bayan tura sakamakon zabe ta hanyar intanet
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Tsohon gwamnan jihar Kaduna kuma jigo a jam’iyyar ADC, Malam Nasir El-Rufai, ya bayyana cewa ba za su yi amfani da tsarin karba-karba a jam'iyyar hadaka ba.
El-Rufai ya jaddada cewa duk wanda ke da niyyar tsayawa takarar shugaban kasa a ƙarƙashin inuwar jam’iyyar ADC zai samu dama, ba tare da takura ko fifita wani yanki ba.

Source: Twitter
ADC za ta bi tsarin karba-karba a 2027?
El-Rufai ya bayyana hakan ne a wata hira ta musamman da ya yi da tashar Trust TV a shirin mintuna 30, inda ya yi bayani kan dabarun ADC na fitar da ɗan takararta da kuma yadda jam’iyyar ke shirin karbe mulki daga hannun APC.
A cewarsa, ADC ta yanke shawarar gudanar da zaɓen fitar da gwani na gaskiya kuma a bude, ba tare da tsarin yanki ko tilasta ɗan takara ta hanyar yarjejeniya ba.
“Ba za mu yi amfani da tsarin karba-karba ba, ba za mu bi wannan hanya ba. Kowa zai samu damar tsayawa takara, kuma duk wanda ya yi nasara, kowa zai mara masa baya,” in ji El-Rufai.
Manyan jiga-jigan da ke neman takara a ADC sun hada da tsohon Mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi.
Jam'iyyar ADC na shirye-shirye a bayan fage
Da yake mayar da martani kan ra’ayin wasu cewa ADC ba ta cika fitowa fili ba duk da ƙorafe-ƙorafen jama’a kan halin da ƙasar ke ciki, El-Rufai ya ce jam’iyyar na yin shirye-shirye ne a hankali, maimakon hayaniya a kafafen yaɗa labarai.
Ya bayyana cewa sabanin APC a shekarar 2014 wadda ta kasance haɗakar jam’iyyu, ADC haɗakar mutane ce, lamarin da ke buƙatar lokaci wajen daidaita tsari da gina ƙaƙƙarfan tubali.
“Akwai ayyuka da dama da ake yi a bayan fage. Ana wayar da kai sosai a matakin ƙasa, ko da yake ba lallai ne a ga komai a kafafen labarai ba,” in ji shi.

Source: Twitter
El-Rufai ya ƙara da cewa jam’iyyar ADC ta fara rajistar mambobi, sannan za ta gudanar da tarukan zaben shugabanni tun daga mazabu, ƙananan hukumomi, kafin a kai ga babban taron ƙasa.
El-Rufai ya goyi bayan zanga-zanga
A wani rahoton, kun ji cewa Malam Nasir El-Rufai ya nuna goyon bayansa ga zanga-zangar da jagororin 'yan adawa suka gudanar a majalisar tarayya kan dokar zabe.

Kara karanta wannan
Tun kafin a yi nisa, an sauke gwamna daga matsayin shugaban kwamitin taron APC na kasa
Tsohon gwamnan na Kaduna ya kuma bayyana gabar da ake tafka magudin zabe a Najeriya, inda ya nuna muhimmancin tura sakamako ta intanet.
El-Rufai ya ce da yana nan da ya shiga zanga-zangar da suka gudanar a majalisar tarayya kan kin amincewa da tanadin tura sakamakon zaɓe ta yanar gizo kai tsaye.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

