Rikicin Rivers; Fadar Shugaban Kasa Ta Sace Gwiwoyin Wike kan Takaddamarsa da Fubara
- Ana ci gaba da muhawara kan rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa dangane da siyasar jihar Rivers mai arzikin mai
- Fadar shugaban kasa ta fito ta yi tsokaci kan rikicin siyasar wanda ya sa alaka ta yi tsami tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Nyesom Wike
- Hadimin Shugaba Tinubu ya bayyana cewa shugaban kasar yana kan matsayar da Nentawe Yilwatda ya dauka dangane da matsayin Gwamna Fubara
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Daniel Bwala, mai ba Shugaba Bola Ahmed Tinubu shawara ta musamman kan yada manufofi, ya yi magana kan rikicin siyasar jihar Rivers.
Daniel Bwala ya ce Shugaba Bola Tinubu ya gamsu da matsayar shugaban jam'iyyar APC na kasa, Nentawe Yilwatda, kan tsarin shugabanci a jihar Rivers.

Source: Facebook
Hadimin shugaban kasar ya bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi a shirin 'Hard Copy' na tashar Channels tv.
Ana yunkurin tsige Gwamna Fubara
Maganar Bwala na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar Dokokin Jihar Rivers ke ci gaba da yunkurin tsige Gwamna Siminalayi Fubara .
Haka kuma an yi musayar kalamai tsakanin Gwamna Fubara da tsohon gwamnan jihar, Nyesom Wike.
Fubara ya samu goyon baya
Daniel Bwala ya ce dole ne a bar gwamna ya gudanar da ayyukansa ba tare da katsalandan ko matsin lamba ba.
Ya ƙara da cewa tasirin siyasar Wike a jihar Rivers ya tsaya ne kawai a cikin jam’iyyar PDP.
“Ina goyon bayan abin da shugaban APC na ƙasa ya faɗa cewa a jihar Rivers, Gwamna Fubara shi ne jagoran APC. Wike ba mamba ne na APC ba, don haka ba zai iya magana da yawun jam’iyyar ba."
"Ana iya kallon Wike a matsayin jagora a cikin PDP a jihar Rivers, kasancewarsa tsohon gwamna, amma jagoran APC a jihar Rivers shi ne Gwamna Fubara.”

Kara karanta wannan
Lissafi zai iya canzawa, Tinubu ya shiga ganawa da gwamnan PDP a fadar shugaban kasa
- Daniel Bwala
Tinubu na goyon bayan matsayar shugaban APC
Bwala ya ce matsayar Shugaba Tinubu ta yi daidai da dokokin cikin gida na jam’iyya da kuma ƙa’idojin dimokuraɗiyya.
“Abin da shugaban jam’iyya ya faɗa shi ne matsayar da shugaban kasa ya tsaya a kai, domin yana girmama dokokin jam’iyya. Shugaban ƙasa yana mutunta doka da bin ƙa’ida, kuma jam’iyya za ta ci gaba da yin hakan."
- Daniel Bwala

Source: Twitter
Me aka ce kan Wike?
Bwala ya kuma taɓo batun koke-koken da ake yi kan tasirin Wike a gwamnatin tarayya, inda ya ce nadin mukamai ba ya fifita muradun kasa.
“Mun ji mutane na cewa kasancewar Wike mamba a majalisar ministoci yana samun wasu fa’idoji."
"An riga an saka wa Wike yadda ya kamata. Shugaban kasa yana son ya saka wa mutane da alheri, amma ba zai taɓa yin abin da zai cutar da muradun Najeriya ba. Shugaba Bola Tinubu yana da sassauci, amma idan ka ketare iyaka, za ka sani.”
- Daniel Bwala
Shirin tsige Fubara ya gamu da cikas
A wani labarin kuma, kun ji cewa yunkurin 'yan majalisar dokokin jihar River na tsige Gwamna Siminalayi Fubara ya gamu da cikas.
Babban alkalin jihar Rivers, Mai shari'a Simeon Amadi ya ƙi amincewa da buƙatar majalisar kan kafa kwamiti domin binciken Gwamna Fubara da mataimakiyarsa, Farfesa Ngozi Odu, bisa zargin aikata manyan laifuffuka.
Mai shari’a Amadi ya sanar da shugaban majalisar dokokin cewa doka ta hana shi daukar irin wannan mataki, saboda akwai umarnin kotu.
Asali: Legit.ng

