Jerin Kwamishinoni da Hadiman Abba da aka Hango a Taron Gidan Kwankwaso

Jerin Kwamishinoni da Hadiman Abba da aka Hango a Taron Gidan Kwankwaso

  • Yayin da siyasar Kano ta ɗauki zafi, an hango manyan jagororin Kwankwasiyya da ke gwamnatin Abba a taron gidan Rabi’u Musa Kwankwaso
  • Taron ya zo a lokacin da ake ta jita-jitar yiwuwar sauya sheƙar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, zuwa APC lamarin da Kwankwaso ya yi tir da shi
  • Haka kuma taron na zuwa a lokacin da Kwankwaso ke kalaman na rashin nasara a cin amana da neman a ba wa Gwamnan shawara kan sauya sheka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

Jihar Kano – Masu rike da mukamai gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf sun halarci wani babban taro da tsohon dan takarar Shugaban Ƙasa, Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi a gidansa.

Wasu daga cikin jagororin Kwankwasiyya da masu muƙamai da aka gani a taron gidan jagoran NNPP na ƙasa, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso, sun haɗa da manyan ’yan siyasa da masu rike da muƙamai a gwamnati da jam’iyya.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya fadi baiwarsa da abin da ya bambanta shi da sauran ƴan siyasa

Yan Kwankwasiyya sun hallara a gidan Kwankwaso
Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso tare da jiga-jigan Kwankwasiyya da ke gwamnatin Abba Hoto: Hon Saifullahi Hassan
Source: Facebook

Arewa Updates ta wallafa sunayen mutane akalla 35 da suke rike da kujeru daban-daban a gwamnatin Abba duk da dambarwar siyasa a Kwankwasiyya a shafin Facebook.

Masu mukaman gwamnatin Kano a taron Kwankwaso

Taron ya jawo ce-ce-ku-ce sosai, musamman ganin lokacin da aka yi shi, wato a yayin da ake ta rade-radin sauya sheƙar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, zuwa jam’iyyar APC.

Jerin sunayen da aka gani a taron sun hada da:

1. Hon. MB Aliyu, Dan Majalisar Jiha mai wakiltar Nasarawa

2. Abdullahi Musa Shugaban Ma’aikatan Kano

3. Musa Gambo Danzaki Sakataren Hukumar Tallafin Karatu ta Kano

4. Sadiq Muhammad Kura Shugaban gidan Zoo

5. Dr. Mansur Hassan Shugaban Kwankwasiyya Scholars

6. Hamisu Dogonnama MD, Kasuwar Kwari

7. Haj. A’in Jafaru Fagge SSA kan yaɗa ayyukan gwamnati

Kwamishinoni sun halarci taron gidan Kwankwaso
Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso tare da Kwamishina a gwamnatin Abba a wani taro a gidansa Hoto: Hon. Saifullahi Hassan
Source: Facebook

8. Haj. Fatima Amneef Shugabar hukumar KASPA

9. Ibrahim Ma’aji Sumaila SSA kan al'amuran ɗalibai

Kara karanta wannan

Abin da Kwankwaso da Ganduje suka fadawa Abba ana batun shigarsa APC

10. Hon. Isyaku Ali Danja SA kan batutuwan majalisa

11. Hon. Shakoor Yassar Shugaban CRC Kano

12. Balarabe Zawachiki, Shugaban Lafiya Jari

13. Sunusi Surajo Kwankwaso (SA, kan al'amuran siyasa

14. Habib Saleh Mailemo Shugaban Kano Pro-Pa

15. Usman Nura Getso PA a ofishin mataimakin Gwamna

16. Aisha Muhammad Idris SA kan samarda wadatar abinci

17. Sadiya Abdu Bichi, SA kan al'amuran mata, yara da masu buƙata ta musamman

18.Sadiya Umar Bichi, Mamba a KSCPC

19. Abdullahi Namama, mashawarci kan al'amuran gwamnati

20. Hamza Ahmad Telan Mata, PA a kan daukar hoto a ofishin mataimakin Gwamna

21. Shafa’atu Ahmad LondonBe (SSR, Ma'aikatar ci gaban karkara

22. Meenan Kwankwasiyya SSR a ma'aikatar matasa da wasanni

23. Inuwa Kwankwaso SSR, KNUPDA

24. Sulaiman Mainasara SSR, kankare zaizayar ƙasa

25. Yusuf Sulaiman Karkasara SSR, KSIP

26. Dr. Yusuf Kofar Mata,Kwamishinan Kimiyya da Fasaha

27. Adamu Aliyu Kibiya,Kwamishinan Agaji da Jinkai

28. Amina Abdullahi HOD,Kwamishinar Al'amuran Mata

29. Mustapha Kwankwaso,Kwamishinan Matasa da Wasanni

Kara karanta wannan

Dalilanmu na son Kwankwaso ya ja Abba zuwa APC inji Hadimin Gwamna Alhajiji Nagoda

30. AVM Ibrahim Umar,Kwamishinan Tsaron Cikin Gida

31. Hon. Hamza Kachako,Kwamishinan Ma'adinai

32. Sani Adamu Wakili, 'Dan Majalisar Wakilai, Minjibir/Ungogo

33. Abdulhakim Kamil Ado, 'Dan Majalisar Wakilai, Wudil/Garko

34. Datti Yusuf Kura, 'Dan Majalisar Wakilai, Kura/Madobi/Garunmalam

35. Hon. Muntari Yarima, 'Dan Majalisar Wakilai, Tarauni

Ra'ayin jama'a game da siyasar Kano

Jama'a sun bayyana mabambantan ra'ayoyi game da mutanen da suka halarci taron Kwankwaso, inda Isma’ila Abubakar Ahmad ya ce:

“To me ya ruwan ku, wallahi ku munafukai ne.”

Amina Muhd ta bayyana cewa:

“Ba laifi ba ne su je, idan ma Abba ya kira taro gobe za su je.”

Kwankwaso ya faɗi bambancinsa da sauran ƴan siyasa

A baya, mun wallafa cewa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa shi ba ɗan siyasa ba ne da ke da farashi ko abin da za a iya sayensa da kuɗi ba.

Ya faɗi hakan ne yayin da yake tsokaci kan halin siyasar Najeriya a baya-bayan nan, musamman a daidai lokacin da ake zargin yiwuwar sauya sheƙar Gwamnan Kano.

Kara karanta wannan

Kwankwaso ya fito da abubuwan alheri da ya yi wa Abba Kabir a baya

Kwankwaso ya ce siyasa tana cike da riba da asara, amma ya jaddada cewa cin amana abu ne da ke janyo fushin jama’a da kuma rasa amincewarsu a kowace irin tafiya.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng