Jigo a PDP Ya Hango Yadda Wike zai Ci Amanar Bola Tinubu da APC

Jigo a PDP Ya Hango Yadda Wike zai Ci Amanar Bola Tinubu da APC

  • Jigo a PDP mai hamayya, Emmanuel Ogidi, ya zargi APC da bai wa Nyesom Wike kwangilar rusa jam’iyyar adawa
  • Ogidi ya ce amma yana da yakinin Wike zai iya juya wa APC baya nan gaba saboda yadda aka ba shi dama
  • Ogidi ya yi wannan batu ne bayan rikici ya ɓarke tsakanin Wike da Sakataren APC na ƙasa, Ajibola Basiru, kan batun Ribas

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.

FCT Abuja – Wani jigon jam’iyyar PDP, Emmanuel Ogidi, ya zargi jam’iyyar APC da ƙarfafa wa Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike gwiwa don rusa yan adawa.

Sai dai Ogidi ya bayyana imanin cewa nan ba da jimawa ba Wike zai iya juyawa jam’iyya mai mulki baya tare da yi mata lahani.

Kara karanta wannan

Hadimin Abba ya fadi abin da ke shirin kora 'yan Kwankwasiyya zuwa jam'iyyar APC

Ana zargin Wike zai ci amanar Tinubu
Ministan Babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike da Shugaban Najeriya Bola Tinubu Hoto: Nyesom Ezenwo Wike
Source: Twitter

Channels TV ta wallafa cewa Ogidi ya bayyana haka ne a ranar inda ya ce zai yi wahala a yi sulhu da mutumin da aikinsa kawai ya rusa jam’iyyarku.

Jagora a PDP ya soki Nyesom Wike

Babban 'dan na PDP ya kara da gargadin cewa babu batun sulhu da Nyesom Wike saboda zargin yana son rusa jam'iyya.

Ya ce:

“Ta ya ya za ka yi sulhu da mutane? Ta yaya za ka yi sulhu da mutumin da ke son rushe gidanka? Ka kalli APC yanzu. Bayan duk hayaniyar da ake yi, su ne suka ba shi ƙarfi domin ya yi ƙoƙarin rusa PDP.”

Ogidi ya ƙara da cewa duk abin da Wike ya yi, zai iya dawowa ya shafi APC ɗin kanta, kuma za ta iya samun matsala saboda haka.

A kalamansa:

“Ya riga ya yi abin da ya yi. Yanzu kuma zai iya juya wa kansu."

Kara karanta wannan

An fadi shekarun da mulki zai yi a Kudu kafin ya dawo yankin Arewa

Yadda Wike ya dagula jam'iyyar PDP

Idan za a iya tunawa Nyesom Wike ya yi aiki da APC a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, inda ya mara wa jam’iyyar baya duk da kasancewarsa ɗan PDP a wancan lokaci.

Tsohon gwamnan Jihar Ribas ya bayyana cewa rashin bin dokokin jam’iyya ne ya sa aka fitar da Atiku Abubakar a matsayin ɗan takarar PDP a zaɓen.

Jagora a PDP ta zargi Aike da lalata jam'iyya
Ministan Abuja, Nyesom Ezenwo Wike Hoto: Lere Olayinka
Source: Facebook

Daga bisani, Wike ya samu naɗin Ministan Abuja, lamarin da ya ƙara rikitar da alaƙarsa da jam’iyyun siyasa.

Wike ya hango karshensa a siyasa

A baya, mun wallafa cewa Nyesom Wike, ya ce duk wani yunƙuri na bai wa Gwamnan Jihar Rivers, Siminalayi Fubara, wa’adi na biyu a 2027 zai jefa siyasar sa cikin mummunan hali.

Wike ya bayyana cewa irin wannan abu zai iya kawo ƙarshen tasirinsa a siyasar jihar Rivers da ma kasa baki ɗaya Saboda haka ya ja daga da duk yunkurin Fubara na sake neman mulki.

Kara karanta wannan

Dalilanmu na son Kwankwaso ya ja Abba zuwa APC inji Hadimin Gwamna Alhajiji Nagoda

Wike ya fadi hakan ne a ranar Asabar, 3 ga watan Disamban 2025, yayin da yake jawabi ga masu ruwa da tsaki na siyasa a wani taro da aka gudanar a karamar hukumar Okrika, a Jihar Rivers

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Ahmad avatar

Aisha Ahmad (Hausa editor) Edita ce a sashen Hausa na legit.ng. Ta samu horon aikin jarida, musamman ta bangaren tace labarai a Premier Radio, da ICIR, da Express Radio. Ta shafe sama da shekaru goma tana aikin ɗaukar rahoto a jihar Kano. aisha.ahmad@corp.legit.ng