"Ba Zan Taba Komawa APC ba," Sanata Ya Yi Kaca Kaca da Gwamnoni 6 a Najeriya

"Ba Zan Taba Komawa APC ba," Sanata Ya Yi Kaca Kaca da Gwamnoni 6 a Najeriya

  • Sanata Enyinnaya Abaribe ya nesanta kansa da batun sauya sheka zuwa jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya da rinjaye a majalisa
  • Dan Majalisar dattawa mai wakiltar Abia ta Kudu ya caccaki gwamnatin Tinubu saboda wahala da kuncin rayuwa da jama'a ke fuskanta
  • Abaribe ya yi ikirarin cewa babu ta yadda shugaban kasa, Bola Tinubu zai samu nasara a 2027 domin mutane sun shirya kayar da shi

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Sanata ami wakiltar Kudancin Abia a Majalisar Dattawan Najeriya, Enyinnaya Abaribe, ya bayyana cewa ba zai taɓa tunanin sauya sheƙa zuwa APC mai mulki ba.

Kalaman Sanata Abaribe na zuwa ne a daidai lokacin da gwamnoni, sanatoci da yan Majalisar Wakilai ke ci gaba da tururuwar komawa APC.

Sanata Abaribe.
Sanata mai wakiltar Kudancin Abia a Majalisar Dattawa, Enyinnaya Abaribe Hoto: Enyinnaya Abaribe
Source: Twitter

Da yake jawabi a cikin shirin Politics Today na tashar Channels ranar Litinin, Sanata Abaribe ya ce ba zai taba bin zugar masu sheka zuwa jam'iyya mai mulki ba

Kara karanta wannan

"Ba za su iya ba": Sanata ya karya lagon masu goyon bayan Shugaba Tinubu

A baya-bayan nan, gwamnonin jihohin shida da suka hada da Akwa Ibom, Bayelsa, Enugu, Delta, Ribas da Taraba sun fice daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC.

Sanata Abaribe ya nesanta jansa da APC

“Idan har akwai wanda zai sauya sheƙa zuwa APC, ina ganin ni ne zan zama na ƙarshe-ƙarshe. A ranar da zan sauya sheƙa, hakan na nufin ba wata jam’iyya da ta rage a Najeriya, har da APC kanta.”
“Ku tambayi kanku, a duk jihohin da ake samun sauya sheƙa, me ke faruwa a can? Waɗannan gwamnonin 'yan adawa ne, sun yi aiki tuƙuru wajen adawa da Tinubu a zaɓen 2023.
"Sai kuma ga shi kwatsam sun sauya sheƙa, kuma an mika jam’iyyar a hannunsu. Ya kamata ku yi wa kanki alkalanci a kan haka."

- Sanata Abaribe.

Abaribe ya koka kan kuncin da mutane ke ciki

Tsohon mataimakin gwamnan jihar Abia ya koka kan tsananin wahala da kuncin rayuwa da ’yan Najeriya ke fuskanta a halin yanzu karkashin mulkin APC.

Kara karanta wannan

"Bai ci zabe ba a 2023": Sanata ya hango makomar Tinubu a zaben 2027

Abaribe ya yi ikirarin cewa al’ummar Najeriya sun ƙara shiri kuma sun ƙuduri aniyar tabbatar da cewa Shugaba Bola Tinubu bai koma kan karagar mulki bayan 2027 ba.

Jam'iyyar APC.
Tutar jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya Hoto: OfficialAPCNig
Source: Twitter

Sanatan ya kuma ce tattalin arzikin ƙasa ya durƙushe ƙarƙashin mulkin Tinubu, tare da cewa har yanzu shugaban bai warware matsalar tsaro ba, in ji rahoton Vanguard.

Ya karkare da cewa babu ta hanyar da Shugaba Tinubu zai samu kuri'un da za su sake ba shi nasara a zaben 2027 idan aka duba halin da jama'a ke ciki.

An yi wa Sanata Natasha tayin APC

A wani rahoton, kun ji cewa Sanata Natasha Akpoti ta bayyana cewa wasu hadimai daga fadar shugaban kasa aun mata tayin sauya sheka APC mai mulkin kasa.

Natasha ta jaddada cewa babu wata barazana ko zuga da za ta sa ta koma APC, tana cewa kasancewarta a jam’iyyar a baya ba ita ce hujjar da zai ta koma jam'iyyar ba.

Ta kuma tabo batun wahalhalu da kalubalen da take fuskanta a rayuwarta, ta yi kira ga mata yan uwanta su ci gaba jajircewa a duk halin da suka tsinci kansu a ciki.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262