Awanni 24 bayan Ganawa da Tinubu, Gwamna Fubara Ya Fice daga PDP zuwa APC
- Gwamna Siminalayi Fubara ya sanar da sauya shekarsa daga PDP zuwa jam'iyyar APC mai mulki a yau Talata, 9 ga watan Disamba, 2025
- Fubara ya ce ya yanke shawarar barin PDP ne saboda ta gaza ba shi kariya musamman a rikicin siyasar da ya auku a jihar Ribas
- Wannan sauya sheka na zuwa ne awanni 24 bayan gwamnan ya ziyarci Shugaba Bola Tinubu a fadar shugaban kasa da ke Abuja
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Rivers, Nigeria - Gwamnan Jihar Ribas, Siminialayi Fubara, da duka magoya bayansa sun yi watsi da jam’iyyar PDP, sun sauya sheka zuwa APC mai mulkin Najeriya.
Hakan na zuwa ne sa'o'i 24 bayan Gwamna Fubara ya ziyarci Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, a fadar gwamnatin tarayya, Abuja.

Source: Facebook
Gwamna Fubara ya tabbatar da sauya sheka zuwa APC ne yayin da yake jawabi a taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a fadar gwamnatin Ribas da ke Fatakwal, in ji Vanguard.
Dalilin Gwamna Simi Fubara na barin PDP
Fubara ya ce fita daga PDP a wurinsa ya zama dole saboda jam'iyyar ta kasa kare shi a rikicin siyasar da ta auku a jihar Ribas har sai da Shugaba Tinubu ya shiga tsakani ya kare shi daga tunbuke shi daga kujerar gwamna.
Gwamnan ya ce duka magoya bayansa sun amince da wannan shawara da ya yanke ta komawa APC saboda a cewarsu, hakan zai ba su damar marawa Shugaba Bola Tinubu baya a 2027.
A kalamansa, Fubara ya ce:
“Abin da ku ka dade kuna jira ya zo. Mun samu cikakken goyon bayan barin wurin da muke, domin ba mu samu wata kariya ba. Idan ba dan Shugaban Ƙasa ba, da yanzu ba za a kira ni gwamna ba.”
“Mu da magoya bayanmu, mun yanke shawara, daga yau mun koma jam'iyyar APC.”
Gwamna Fubara ya goyi bayan Tinubu
Da yake tsokaci kan dalilin zuwansa fadar shugaban kasa da ganawa da Bola Tinubu, Gwamna Fubara ya ce ziyarar tana da alaka da goyon bayan tazarcensa a 2027.
Ya ce ya shaida wa Shugaba Tinubu cewa shi da magoya bayansa suna tare da shi, kuma za su yi aiki domin ganin ya cimma burinsa na tazarce zuwa wa'adi na biyu a zabe mai zuwa.
Fubara ya kara da cewa ba zai iya mara wa Tinubu baya gaba ɗaya ba muddin yana PDP, shi ya sa dole shi da duka magoya bayansa su hade da APC, kamar yadda Daily Trust ta rahoto.

Source: Facebook
Fubara ya kara yabon Bola Tinubu
A wani rahoton, kun ji cewa gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara, ya yi godiya na musamman ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu bayan dawo da shi kan kujerarsa da ya shafe watanni shida ba ya kai.
Fubara ya ce cigaba da rike mukaminsa bayan dokar ta-baci ta watanni shida ya samu ne saboda tagomashi na musamman da alfarma daga Shugaba Bola Tinubu.
Gwamnan ya tabbatar da cewa gwamnati za ta koma cikakken aiki, kuma duk korafe-korafen da jama'a suka gabatar za a magance su nan ba da jimawa ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

