Umar: 'Wike Ya Gindaya Sharadi Mai Tsanani kafin a Samu Zaman Lafiya a PDP

Umar: 'Wike Ya Gindaya Sharadi Mai Tsanani kafin a Samu Zaman Lafiya a PDP

  • Wani jigon PDP, Umar Sani ya ce Nyesom Wike ya bukaci jam'iyyar da ta hakura da takarar shugabancin kasa a 2027
  • A cewar Umar, hakura da takarar ne sharadin sulhu da ministan Abuja ya ba PDP, tare da barazanar sake jefa ta a rikici
  • Jigon ya kuma yi magana game da rashin halartar jihohin Rivers, Osun da Taraba babban taron PDP da aka gudanar

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida

Abuja - Wani babban jigon PDP, Umar Sani, ya bayyana cewa sharadin sulhu da ministan Abuja, Nyesom Wike, ya gindaya wa jam’iyyar gabanin 2027.

Umar Sani ya ce Wike ya umarci PDP da ta amince ba za ta tsayar da dan takarar shugaban kasa ba a 2027 idan har jam'iyyar na son kwanciyar hankali.

Jigon PDP ya ce Wike ya ginda wa jam'iyyar sharadin hakura da takarar shugabancin kasa a 2027
Hoton ministan Abuja, Nyesome Wike da na matashi rike da tutar jam'iyyar PDP. Hoto: @GovWike/Kola Sulaiman
Source: UGC

Wike na so PDP ta hakura da takara a 2027

Kara karanta wannan

Ran APC ya baci, ta dura kan PDP bayan saboda taimakon Trump a Najeriya

A zantawarsa da jaridar Daily Independent, Umar Sani ya bayyana cewa Wike ya fadi hakan ne lokacin da kwamitin sulhu da BoT ta kafa ya kai masa ziyara domin sasanci.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewarsa, Wike ya bayyana cewa za a samu rikici mai muni idan PDP ta tsayar da dan takarar shugaban kasa domin kalubalantar Shugaba Bola Tinubu a 2027.

Umar Sani ya ce bayan ganin wannan matsaya ta Wike, jam’iyyar ta fahimci cewa babu wata hanyar sulhu da za ta yiwu, saboda sharuddan nasa sun sabawa manufa da tsarin jam’iyyar.

Saboda haka, Umar Sani ya ce PDP yanke hukunci cewa cire shi daga jam’iyyar ya zama dole duk da cewa an yi hakan ne a makare.

Yadda rikicin ya shafi taron PDP a Ibadan

Umar Sani ya ce rikicin cikin gida ya bayyana sosai a babban gangamin PDP da aka gudanar a Ibadan, inda wasu jihohi ba su halarta ba.

Ya ce jihohin Osun, Taraba da Rivers ba su turo wakilai ba, haka ma gwamnoninsu ba su halarta ba. Wannan, a cewarsa, ya nuna irin gagarumar matsalar da jam’iyyar ke fama da ita.

Kara karanta wannan

Ana wata ga wata: PDP ta fatattaki Gwamna Bala da wasu gwamnoni 2 daga jam'iyyar

Ya ce wannan rashin halarta daga manyan jihohi ya janyo dimuwa a cikin jam’iyya, musamman ganin cewa 2027 na tafe kuma har yanzu PDP ba ta da cikakken tsari ko hadin kai.

Jigon na PDP ya bayyana cewa yanayin da jam'iyyar ta fada a halin yanzu shi ne mafi muni tun kafuwarta, saboda rashin zaman lafiya ya hana jam’iyyar sake farfado da martabarta.

Umar Sani PDP
Hoton wani bangare na babban taron jam'iyyar PDP da aka gudanar a Ibadan, jihar Oyo. Hoto: @OfficialPDPNig
Source: Twitter

Korar kusoshi za ta sake rikita PDP

Babban jigon na PDP ya ce korar manyan jiga-jigai daga jam’iyyar, ciki har da Nyesom Wike, Ayo Fayose da Samuel Anyanwu, zai kara tsananta rashin kwanciyar hankali.

Ya ce wadannan mutanen suna da girman tasiri a jam’iyyar, kuma rashinsu su zai iya janyo durkushewar PDP gaba ɗaya.

Ya yi tambaya kan yadda jam’iyyar za ta iya jure guguwar shari’u, rarrabuwar kawuna, da rashin amincewa na cikin gida da ke ci gaba da danne ta gabanin 2027.

PDP ta kori gwamnoni 3 daga jam'iyyar

A wani labarin, mun ruwaito cewa, PDP ta tabbatar da korar gwamnoni uku da tsofaffin jagorori saboda aikata wasu laifuffuka da suka sabawa jam'iyya.

Kara karanta wannan

Abu ya kacame, sabon shugaban PDP da tsagin Wike na iya arangama a taro

Jam'iyyar da ke karkashin tsagin ministan Abuja, Nyesom Wike, ta ce ta kori gwamnonin da kuma kusoshin ne domin dawo da martabar PDP.

Hakazalika, PDP ta sanar da tsige dukkanin shugabanninta a jihohi shida tare da ba kwamitin NWC umarnin kafa shugabannin riko kafin a yi zabe.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com